< Lukas 8 >

1 Och det begaf sig derefter, att han vandrade i städer och byar, predikade och förkunnade Evangelium om Guds rike; och de tolf med honom;
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 Dertill några qvinnor, som han hade helbregda gjort ifrå de onda andar och krankheter, nämliga: Maria, som kallas Magdalena, af hvilka sju djeflar utgångne voro;
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 Och Joanna, Chuse hustru, Herodis fogdes, och Susanna, och många andra, som honom tjente af sina ägodelar.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Då nu mycket folk kom tillhopa, och utaf städerna sökte till honom, talade han genom liknelse:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 En sädesman gick ut till att så sina säd; och vid han sådde, föll somt vid vägen, och vardt förtrampadt, och foglarna under himmelen åto det.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Och somt föll på hälleberget, och då det uppgick, förtorkades det; ty det hade ingen vätsko.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Och somt föll ibland törne, och törnen gingo med upp, och förqvafde det.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 Och somt föll i goda jord; och det gick upp, och gjorde hundradefald frukt. Då han detta sade, ropade han: Den der hafver öron till att höra, han höre.
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Då frågade honom hans Lärjungar, hurudana denna liknelsen var.
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 Han sade till dem: Eder är gifvet veta Guds rikes hemlighet, men dem androm genom liknelse; på det att, ändock de se, skola de likväl icke se, och ändock de höra, skola de likväl icke förstå.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Så är nu denna liknelsen. Säden är Guds ord;
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 Men de som vid vägen, det äro de som höra; sedan kommer djefvulen, och tager bort ordet utu deras hjerta, att de icke tro skola, och blifva frälste.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Men de som på hälleberget, det äro de som, när de höra, anamma de ordet med glädje, och de hafva inga rötter; de der tro till en tid, och då frestelsen påkommer, falla de derifrå.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Men det som föll ibland törnen, äro de som höra; och gå bort, och varda förqvafde af omsorger, och rikedomar, och lifsens vällust; och bära ingen frukt.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Men det uti goda jord, äro de som höra ordet, och behålla det uti ganska godt hjerta; och bära frukt i tålamod.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Men ingen upptänder ett ljus, och skyler det under något kar, eller sätter under bänken; utan sätter det på ljusastakan, att de, som ingå, skola få se ljuset.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Ty det är intet lönligit, som icke skall varda uppenbart; och intet fördoldt, det icke skall kunnigt varda, och uppkomma skall i ljuset.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Ser fördenskull till, huru I hören; ty den der hafver, honom varder gifvet, och den der intet hafver, det han menar sig hafva, det skall ock tagas ifrå honom.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Så gingo till honom hans moder och hans bröder; och kunde dock icke komma till honom, för folkets skull.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 Då vardt honom bådadt, och sagdt: Din moder och dine bröder stå härute, och vilja se dig.
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 Svarade han, och sade till dem: Min moder och mine bröder äro desse, som höra Guds ord, och görat.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Så begaf det sig på en dag, att han steg uti ett skepp, med sina Lärjungar, och sade till dem: Låt oss fara öfver sjön. Och de lade utaf.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 Sedan, vid de foro öfver, somnade han; och der reste upp ett stort väder på sjön; och de förfylldes, och voro i stor fara.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Så gingo de till, och väckte honom upp, sägande: Mästar, Mästar, vi förgås. Då stod han upp, och näpste vädret och vattnens våg; och så vände det igen, och blef stilla.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 Och han sade till dem: Hvar är edar tro? Men de fruktade, och förundrade, sägandes emellan sig: Ho må denne vara? Ty han bjuder både vädrena och vattnena; och de lyda honom.
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Och de foro till de Gadareners ängd, hvilken är tvärt öfver Galileen.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Och då han utgången var af skeppet på landet, mötte honom en man utaf staden, hvilken hade haft djefvulen i lång tid; och han hade inga kläder på, ej heller blef i husen, utan i grifter.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Då han såg Jesum, ropade han, och föll ned framför honom, och sade med höga röst: Hvad hafver jag göra med dig, Jesu, dens högstas Guds Son? Jag beder dig, att du icke qväl mig.
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 Ty han böd dem orena andanom, att han skulle fara ut af mannenom; ty han hade länge plågat honom; och han vardt bunden i kedjor, och förvarad i fjettrar, och slet sönder banden, och vardt drifven af djefvulen bort i öknen.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Då frågade Jesus honom, och sade: Hvad är ditt namn? Han sade: Legio; ty månge djeflar voro inkomne i honom.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 Och de bådo honom, att han icke skulle bjuda dem fara uti afgrunden. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Men der var en stor svinahjord, som der gick och födde sig på berget. Då bådo de honom, att han ville tillstädja dem fara in i svinen; och han tillstadde dem det.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Då foro djeflarna utu menniskone, och foro in uti svinen; och hjorden brådstörte sig uti sjön, och fördränkte sig.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 Men när de, som vaktade svinen, sågo hvad der skedde, flydde de, och båro tidenden i staden, och på bygdena.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Då gingo de ut, till att se hvad der skedt var, och kommo till Jesum; och funno mannen, der djeflarna utaf farne voro, klädd och vid sin sinne, sittandes vid Jesu fötter; och vordo förfärade.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Och de som det sett hade, förkunnade dem desslikes, huruledes den besatte var helbregda vorden.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Och hele hopen af de Gadareners omliggande bådo honom, att han ville fara ifrå dem; ty dem var en stor räddhåge påkommen. Då steg han till skepps, och for tillbaka igen.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Men mannen, der djeflarna voro utaf farne, bad honom att han måtte blifva när honom. Men Jesus sände honom ifrå sig, sägandes:
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 Gack uti ditt hus igen, och säg utaf, huru stor ting Gud med dig gjort hafver. Och han gick bort, och förkunnade öfver hela staden, huru stor ting Jesus hade gjort med honom.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Och det begaf sig, då Jesus kom igen, undfick honom folket; ty alle vänte efter honom.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 Och si, der kom en man, som het Jairus, och var en öfverste för Synagogon; han föll ned för Jesu fötter, bedjandes honom, att han ville gå i hans hus;
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 Ty han hade ena enda dotter, vid tolf åra gammal, och hon begynte själas; men i vägen, vid han gick dit, trängde honom folket.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Och en qvinna, som blodgång hade haft i tolf år, och hade förtärt allt hvad hon ägde på läkare, och kunde dock botas af ingom;
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 Hon gick bakefter, och tog på hans klädefåll; och straxt stillades hennes blodgång.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 Och Jesus sade: Ho är den, som tog på mig? Då de alle nekade, sade Petrus, och de med honom voro: Mästar, folket tränger dig, och omakar dig, och du säger: Ho tog på mig?
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 Då sade Jesus: Någor hafver ju tagit på mig; ty jag kände, att kraft gick af mig.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 Då qvinnan såg, att det icke var lönligit, kom hon skälfvandes, och föll ned för hans fötter, och förkunnade för allo folkena, för hvad saks skull hon hade tagit på honom, och huruledes hon blef straxt helbregda.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Då sade han till henne: Var tröst, min dotter, din tro hafver frälst dig; gack med frid.
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 Vid han ännu talade, kom en utaf öfverstans hus för Synagogon, sägandes till honom: Din dotter är död; gör icke Mästaren omak.
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Då Jesus hörde det ordet, sade han till pigones fader: Räds intet; utan tro allenast, och hon varder helbregda.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 Då han kom i huset, stadde han ingom ingå med sig, utan Petrum, Jacobum och Johannem, och fadren och modren till pigona.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Men de greto alle, och jämrade sig öfver henne. Då sade han: Gråter icke; pigan är icke död, men hon sofver.
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 Då gjorde de spe af honom, väl vetande att hon var död.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 Men han dref dem alla ut, och tog henne vid handena, och ropade, sägandes: Piga, statt upp.
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Och hennes ande kom igen, och hon stod straxt upp; och han böd gifva henne mat.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Och hennes föräldrar förskräcktes. Men han böd dem, att de ingom säga skulle, hvad der skedt var.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Lukas 8 >