< Lukas 1 >

1 Efter månge hafva tagit sig före att beskrifva de ting, som ibland oss aldravissast äro;
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Såsom de oss sagt hafva, som af begynnelsen det med sin ögon sågo, och sjelfve en del voro af det de sade;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Syntes ock mig, sedan jag af begynnelsen all ting granneliga utfrågat hafver, ordenteligen skrifva dig till, min gode Theophile;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Att du må förfara vissa sanningen om de stycker, der du om undervister äst.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Uti Herodis, Judee Konungs, tid, var en Prest, utaf Abie skifte, benämnd Zacharias; och hans hustru, af Aarons döttrar, benämnd Elisabet.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 De voro både rättfärdige för Gud, vandrande i all Herrans bud och stadgar ostraffeliga.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Och de hade inga barn; ty Elisabet var ofruktsam, och både voro de framlidne i sin ålder.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Så begaf det sig, då han i sitt skifte skulle hålla sitt Prestaämbete för Gudi,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Efter Presterskapets sed, och det föll på honom, att han skulle upptända rökelse, gick han in i Herrans tempel;
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Och allt folket var utantill, och bad, så länge rökelsen skedde.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Så syntes honom Herrans Ängel, ståndandes på högra sidon vid rökaltaret.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Och Zacharias vardt förskräckt, då han såg honom, och en räddhåge föll öfver honom.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Så sade Ängelen till honom: Var icke förfärad, Zacharia; ty din bön är hörd, och din hustru Elisabet skall föda dig en son, hvilkens namn du skall kalla Johannes.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Och dig skall varda glädje och fröjd; och månge skola fröjdas af hans födelse;
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Ty han skall varda stor för Herranom; vin och starka drycker skall han icke dricka; och skall straxt i moderlifvet uppfylld varda med den Helga Anda;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Och han skall omvända många af Israels barn till Herran, deras Gud.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Och han skall gå för honom, med Elie anda och kraft, till att omvända fädernas hjerta till barnen, och de ohöriga till de rättfärdigas snällhet; och göra Herranom ett beredt folk.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Då sade Zacharias till Ängelen: Hvaraf skall jag detta veta? Ty jag är gammal, och min hustru är framliden i åldren.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Ängelen svarade, och sade till honom: Jag är Gabriel, som står i Guds åsyn, och är utsänd till att tala dig till, och båda dig denna goda tidenden.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Och si, du skall varda mållös, och skall intet kunna tala, intill den dagen, då detta sker; derföre, att du icke trodde minom ordom, hvilke skola fullkomnad varda i sin tid.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Och folket förbidde Zachariam, och förundrade sig, att han så länge dvaldes i templet.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Men då han utgick, kunde han intet tala med dem; och så förmärkte de, att han hade sett någon syn i templet; och han tecknade dem, och blef mållös.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Och det begaf sig, då hans ämbetsdagar ute voro, gick han hem i sitt hus.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Och efter de dagar vardt hans hustru Elisabet hafvandes; och fördolde sig i fem månader, och sade:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Så hafver nu Herren gjort med mig, i de dagar, då han såg till mig, på det han skulle borttaga min försmädelse ibland menniskorna.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Uti sjette månaden vardt Gabriel Ängel utsänd af Gudi, uti en stad i Galileen, benämnd Nazareth;
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 Till en jungfru, som förlofvad var enom man, hvilkens namn var Joseph, af Davids hus; och jungfrunes namn Maria.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Och Ängelen kom in till henne, och sade: Hel, full med nåd! Herren är med dig; välsignad du ibland qvinnor.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Då hon såg honom, vardt hon förfärad af hans tal, och tänkte uppå, hurudana helsning detta var.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Då sade Ängelen till henne: Frukta dig icke, Maria; ty du hafver funnit nåd för Gudi.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Si, du skall afla i ditt lif, och föda en son, hvilkens Namn du skall kalla JESUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Han skall varda stor, och kallas dens Högstas Son; och Herren Gud skall gifva honom hans faders Davids säte;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 Och han skall vara en Konung öfver Jacobs hus i evig tid; och på hans rike skall ingen ände vara. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Då sade Maria till Ängelen: Huru skall detta tillgå? Ty jag vet af ingen man.
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Ängelen svarade, och sade till henne: Den Helge Ande skall komma öfver dig, och dens Högstas kraft skall öfverskygga dig; derföre ock det Helga, som af dig födt varder, skall kallas Guds Son.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Och si, Elisabet, din fränka, hafver ock aflat en son i sin ålderdom; och detta är sjette månaden åt henne, som hetes vara ofruktsam;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Ty för Gud är ingen ting omöjelig.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Då sade Maria: Si, Herrans tjenarinna; varde mig efter ditt tal. Och Ängelen skiljdes ifrå henne.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Uti de dagar stod Maria upp, och gick i bergsbygdena med hast, uti Jude stad;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Och kom uti Zacharie hus, och helsade Elisabet.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Och det begaf sig, då Elisabet hörde Marie helsning, sprang barnet uti hennes lif. Och Elisabet vardt uppfylld med den Helga Anda;
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Och hon ropade med höga röst, och sade: Välsignad du ibland qvinnor, och välsignad dins lifs frukt.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Och hvadan kommer mig detta, att mins Herras moder kommer till mig?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Si, då rösten af dine helsning kom i min öron, sprang barnet af glädje i mitt lif.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Och salig äst du, som trodde; ty all ting varda fullbordad, som dig sagd äro af Herranom.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Och Maria sade: Min själ prisar storliga Herran;
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Och min ande fröjdar sig i Gudi, minom Frälsare;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Ty han hafver sett till sine tjenarinnos ringhet: Si, härefter varda all slägte mig saliga kallande.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Ty den Mägtige hafver gjort mägtig ting med mig, och hans Namn är heligt;
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Och hans barmhertighet varar ifrå slägte till slägte, öfver dem som frukta honom.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Han hafver bedrifvit magt med sinom arm, och förskingrat dem, som högfärdige äro uti deras hjertas sinne.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 De mägtige hafver han satt af sätet, och uppsatt de ringa.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 De hungriga hafver han med god ting uppfyllt, och de rika hafver han låtit tomma blifva.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Han hafver upptagit sin tjenare Israel, tänkande på sina barmhertighet;
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 Såsom han sagt hafver till våra fäder, Abraham och hans säd, till evig tid. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Och Maria blef när henne vid tre månader; och gick så hem i sitt hus igen.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Så vardt då Elisabet tiden fullbordad att hon skulle föda, och hon födde en son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Och hennes grannar och fränder fingo höra, att Herren hade gjort stor barmhertighet med henne, och fröjdade sig med henne.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Och det begaf sig, på åttonde dagen kommo de till att omskära barnet; och kallade honom, efter hans fader, Zacharias.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Då svarade hans moder, och sade: Ingalunda; men han skall heta Johannes.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Då sade de till henne: Uti dine slägt är ingen, som hafver det namnet.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Så tecknade de hans fader, hvad han ville kalla honom.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Och han äskade ena taflo, der han uti skref, sägandes: Johannes är hans namn; och alle förundrade sig derpå.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Och straxt öppnades hans mun, och hans tunga; och han talade, lofvandes Gud.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Och stor fruktan kom öfver alla deras grannar; och ryktet om allt detta gick ut öfver alla Judiska bergsbygdena.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Och alle de, som det hörde, sattet i sitt hjerta, sägande: Hvad månn varda utaf detta barnet? Ty Herrans hand var med honom.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Och hans fader Zacharias vardt uppfylld med den Helga Anda, propheterade, och sade:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Lofvad vare Herren, Israels Gud; ty han hafver besökt och förlossat sitt folk;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Och hafver upprättat oss salighetenes horn, uti sins tjenares Davids hus;
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 Såsom han i förtiden talat hafver, genom sina helga Propheters mun; (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Att han skulle frälsa oss ifrå våra ovänner, och utur allas deras hand, som hata oss;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Och bevisa barmhertighet med våra fäder, och minnas på sitt helga Testamente;
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Och på den ed, som han svorit hafver vårom fader Abraham, att gifva oss;
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Att vi, frälste utur våra ovänners hand, måtte honom tjena utan fruktan;
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 I helighet och rättfärdighet, för honom, i alla våra lifsdagar.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Och du barn skall kallas dens Högstas Prophet; du skall gå för Herranom, till att bereda hans vägar;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Och gifva hans folke salighetenes kunskap, till deras synders förlåtelse;
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Genom vår Guds innerliga barmhertighet, genom hvilken uppgången af höjdene hafver oss besökt;
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Till att uppenbaras dem, som sitta i mörkret och dödsens skugga, och styra våra fötter på fridsens väg.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Och barnet växte upp, och stärktes i Andanom; och vistades i öknene, till den dagen han skulle framkomma för Israels folk.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Lukas 1 >