< Jesaja 28 >

1 Ve den stolta kronone, de drucknas af Ephraim, det falnade blomstret, hans lustiga härlighets, hvilket öfver den feta dalen står, deras som af vin raga.
Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
2 Si! en starker och mägtiger af Herranom, såsom en hagelstorm, såsom ett skadeligit väder, såsom en vattustorm, den starkeliga infaller, skall uti landet med våld insläppt varda;
Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
3 Att den stolta kronan, och drucknas af Ephraim, skall med fötter trampad varda;
Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
4 Och det falnade blomstret, hans lustiga härlighets, hvilket öfver den feta dalen står, skall varda såsom det bittida på sommaren mognas, hvilket förgås, medan man ännu ser det hänga på sina qvistar.
Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
5 På den tiden skall Herren Zebaoth vara dem igenlefdom af sitt folk en lustig krona, och en härlig krans;
A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
6 Och en doms ande honom som för rätta sitter, och en starkhet dem som igenkomma af stridene till porten.
Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
7 Dertill äro ock dessa galne vordne af vin, och raga af starkom dryck; ty både Prester och Propheter äro galne af starkom dryck. De äro drunknade uti vin, och raga af starkom dryck; de äro galne i Prophetien, och drabba icke rätt i domen.
Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
8 Ty all bord äro full med spyor, och slemhet allstädes.
Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
9 Hvem skall han då lära vishet? Hvem skall han då låta predikan förstå? Dem afvandom af mjölkene, dem aftagnom ifrå bröstet.
“Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
10 Ty de säga: Bjud, bjud, bjud, bjud; bida, bida, bida, bida, här litet, der litet.
Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
11 Nu väl, han skall en gång med spotskliga läppar och med ett annat tungomål tala till detta folket;
To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
12 Hvilko nu detta predikadt varder: Så hafver man ro, så vederqvicker man de trötta, så varder man stilla; och vilja dock icke höra denna predikanen.
waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
13 Derföre skall dem ock Herrans ord alltså varda: Bjud, bjud, bjud, bjud; bida, bida, bida, bida, här litet, der litet; att de skola gå bort, och falla tillbaka, förkrossas, besnärde och fångne varda.
Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
14 Så hörer nu Herrans ord, I bespottare, som rådande ären öfver detta folk som i Jerusalem är.
Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
15 Ty I sägen: Vi hafve gjort ett förbund med döden, och förvete oss med helvetet. När en flod kommer, skall hon intet drabba på oss; ty vi hafve gjort oss en falsk tillflykt, och gjort oss en bedrägelig skärm. (Sheol h7585)
Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
16 Derföre säger Herren Herren alltså: Si, jag lägger i Zion en grundsten, en pröfvosten, en kostelig hörnsten, den väl grundad är. Den der tror, han skall icke förskräckas.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
17 Och jag skall göra domen till ett rättesnöre, och rättfärdighetena, till en vigt. Så skall haglet drifva den falska tillflykten bort, och vatten skall föra skärmen bort;
Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
18 Att edart förbund med döden skall löst varda, och edart förvetande med helvetet skall icke bestå, och när en flod går fram, skall hon förtrampa eder. (Sheol h7585)
Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
19 Så snart hon framgår, skall hon taga eder bort. Kommer hon om morgonen, så sker det om morgonen; sammalunda, ehvad hon kommer dag eller natt; ty straffet allena lärer gifva akt uppå orden.
A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
20 Ty sängen är för trång, så att intet öfver är, och täckenet så stackot, att man måste krympa sig derunder.
wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
21 Ty Herren skall uppstå lika som på de bergena Perazim, och vredgas, såsom uti Gibeons dal; på det han skall göra sitt verk vid ett annat sätt, och att han sitt arbete göra skall vid ett annat sätt.
Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
22 Så lägger nu bort edart begabberi, på det edor band icke skola hårdare varda; ty jag hafver hört en förderfvelse och afkortelse, den af Herranom, Herranom Zebaoth ske skall i allo verldene.
Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
23 Fatter med öronen, och hörer mina röst; märker åt, och hörer mitt tal.
Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
24 Plöjer eller träder, eller arbetar ock en åkerman sin åker alltid till säd?
Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
25 Är icke så? När han hafver gjort honom jemn, så sår han deruti ärter, och kastar kummin, och sår hvete och bjugg, hvart och ett dit som han det hafva vill, och hafra på sitt rum;
Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
26 Alltså, tuktar ock dem deras Gud med straff, och lärer dem.
Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
27 Ty man tröskar icke ärter med slago, och låter man ej heller vagnshjulet gå öfver kummin; utan ärter slår man ut med en staf, och kummin med ett spö.
Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
28 Man mal det till bröds, och man tröskar det icke alldeles till intet, när man med vagnshjul och hästar uttröskar det.
Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
29 Detta sker ock af Herranom Zebaoth; ty hans råd är underligit, och går det härliga igenom.
Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.

< Jesaja 28 >