< San Lucas 17 >

1 Y dijo a sus discípulos: siempre vendrán oportunidad de pecar, pero Ay! de aquel por quien vienen.
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 Sería bueno para él que le pusieran una gran piedra en el cuello y lo tiraran al mar, antes de que causara problemas a ninguno de estos pequeños.
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 Presten atención a sí mismos: si tu hermano peca contra ti, repréndele; y si se arrepiente de su pecado, perdónale.
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 Y si pecare contra ti siete veces en un día, y siete veces viene a ti y dice: Me arrepiento de lo que he hecho; perdonale.
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 Y los doce dijeron al Señor: incrementa nuestra fe.
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 Y el Señor dijo: Si su fe es como un grano de mostaza, dirían a este árbol: Sé desarraigado y plántate en el mar; y les obedecerá.
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 ¿Y quién de ustedes, teniendo un siervo que está arando o cuidando ovejas, le dirá que cuando entre del campo, venga ahora y se siente y comience a comer,
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 No le dice más bien: prepárame la cena, y prepárate para atenderme hasta que haya comido y bebido; y después de eso, come y bebe tu?
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 ¿Dio gracias al siervo porque hizo lo que se le ordenó? No.
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 De la misma manera, cuando hayas hecho todo lo que se te ha encomendado, digan: No hay mérito en nosotros, porque solo hemos hecho lo que se nos ordenó que hiciéramos.
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 Y aconteció que cuando estaban en el camino a Jerusalén, él pasó por Samaria y Galilea.
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 Y cuando él entró en un pequeño pueblo, se encontró con diez hombres que eran leprosos, y ellos, manteniéndose a distancia,
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 Decían en voz alta, Jesús, Maestro, ten piedad de nosotros!
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 Y cuando los vio, les dijo: vayan, a mostrarse a los sacerdotes para que los vean. Y, mientras iban, se hicieron limpios.
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 Y uno de ellos, cuando vio que estaba limpio, se volvió y alabó a Dios en alta voz;
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 Y, cayendo sobre su rostro a los pies de Jesús, le dio gracias; y él era un hombre de Samaria.
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 Y Jesús dijo: ¿No había diez hombres que fueron limpios? dónde están los nueve?
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 ¿No han vuelto alguno de ellos para dar gloria a Dios, sino sólo éste extranjero?
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 Y él le dijo: Levántate, y sigue tu camino; tu fe te ha sanado.
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Y cuando los fariseos le preguntaron acerca de cuándo vendría el reino de Dios, él les dio una respuesta y dijo: El reino de Dios no vendrá por medio de la observación:
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 Y los hombres no dirán: ¡Mira, ya está aquí! o, ¡allí! porque el reino de Dios está entre ustedes.
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 Y dijo a sus discípulos: El tiempo vendrá cuando desearán ver uno de los días del Hijo del hombre, pero no lo verán.
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 Y si te dicen: ¡Mira, está allí! o, está aquí! no te vayas, o ve tras ellos.
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 Porque como en un relámpago se ve la luz brillante desde un extremo del cielo hasta el otro, así será el Hijo del hombre cuando llegue su hora.
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 Pero primero, tendrá que sufrir mucho y ser rechazado por esta generación.
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 Y como fue en los días de Noé, así será en el día del Hijo del hombre.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 Ellos estaban festejando y tomando esposas y casándose, hasta el día del diluvio de las aguas, cuando Noé entró en el arca, y todos vinieron a la destrucción.
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 De la misma manera, en los días de Lot; estaban festejando y comerciando, plantaban y edificaban;
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 Pero el día en que Lot salió de Sodoma, fuego y azufre del cielo descendió y la destrucción vino sobre todos ellos.
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 Así será en el día de la revelación del Hijo del hombre.
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 En aquel día, si alguno está en el tejado de la casa, y sus bienes están en la casa, que no baje para llevarlos; y el que está en el campo no regrese a su casa.
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 Tenga en cuenta la esposa de Lot.
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 Si alguien intenta mantener su vida, la perderá, pero si alguien renuncia a su vida, la salvará.
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 Les digo que en esa noche habrá dos hombres durmiendo en una cama, y uno será llevado y el otro dejado.
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 Dos mujeres estarán moliendo juntas; una será tomada y la otra llevada.
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
36 Dos estarán en el campo; él uno será tomado y el otro dejado.
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 Y ellos, respondiendo, dijeron: ¿Dónde, Señor? Y él les dijo: Dónde está el cuerpo, allí se juntarán las águilas.
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”

< San Lucas 17 >