< Jueces 18 >

1 En aquellos días no había rey en Israel, y en esos días los danitas buscaban una herencia para sí mismos, para ser su lugar de vida; durante ese tiempo no se les había distribuido tierra entre las tribus de Israel.
To, a kwanakin nan Isra’ila ba ta da sarki. A kwanakin kuwa zuriyar Dan tana neman wurinsu na zama, gama ba su riga sun sami gādo tare da kabilan Isra’ila ba.
2 Entonces los hijos de Dan enviaron a cinco hombres de entre ellos, hombres fuertes, desde Zora y desde Estaol, para espiar y que explorarán la tierra; Y ellos les dijeron: Vayan a espiar y explorar la tierra; y llegaron a la región montañosa de Efraín, a la casa de Micaías, donde hicieron una parada para pasar la noche.
Saboda haka mutanen Dan suka aika jarumawa guda biyar daga Zora da Eshtawol don su leƙi asirin ƙasar su kuma bincike ta. Waɗannan mutanen sun wakilci dukan kabilar. Suka ce musu, “Ku je, ku bincike ƙasar.” Mutanen suka shiga ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika, inda suka kwana.
3 Cuando estaban cerca de la casa de Micaías, oyendo una voz que no era extraña para ellos, la del joven levita, salieron de su camino a su casa y le dijeron: ¿Cómo has venido aquí? y qué haces en este lugar y porque estas aqui.
Sa’ad da suka yi kusa da gidan Mika, sai suka gane muryar saurayin nan Balawe; saboda haka suka shiga wurin suka tambaye shi, “Wa ya kawo ka nan? Me kake yi a nan? Me ya sa kake a nan?”
4 Y él les dijo: Esto es lo que Micaias hizo por mí, y él me pagó y me convertí en su sacerdote.
Ya gaya musu abin da Mika ya faɗa masa ya ce, “Ya ɗauke ni aiki ya kuma sa in zama masa firist.”
5 Luego dijeron: Pregunta dirección de Dios para nosotros, para ver si el viaje en el que vamos tendrá un buen resultado.
Sa’an nan suka ce masa, “Muna roƙonka ka nemi mana nufin Allah don mu sani ko tafiyarmu tana da nasara.”
6 Y el sacerdote les dijo: Vayan en paz; su camino es guiado por el Señor.
Firist ya amsa ya ce, “Ku sauka lafiya, gama tafiyarku tana da yardan Ubangiji.”
7 Luego los cinco hombres siguieron su camino y fueron a Lais y vieron a las personas que estaban allí, viviendo sin pensar en el peligro, como los sidonios, tranquilos y seguros; porque tenían todo en la tierra para sus necesidades, y estaban lejos de los sidonios y no tenían ningún negocio con nadie.
Saboda haka mutum biyar ɗin suka tashi suka iso Layish, inda suka ga mutane suna zamansu a huce, kamar Sidoniyawa, ba sa zato ga tsaro. Kuma da yake ƙasarsu ba ta bukata kome, suna da wadata. Suna kuma nesa da Sidoniyawa, ba sa kuma hulɗa da kowa.
8 Entonces volvieron a sus hermanos en Zora y Estaol, y sus hermanos les dijeron: ¿Qué noticias tienes?
Da suka komo Zora da Eshtawol,’yan’uwansu suka tambaye su, “Me kuka gano?”
9 Y ellos respondieron: ¡Arriba! Y vayamos contra Lais; Porque hemos visto la tierra, y es muy buena: ¿Que esperas, por qué no haces nada? No te demores en entrar y tomar la tierra por tu herencia.
Suka ce, “Ku zo mu yaƙe su! Mun ga ƙasar tana da kyau sosai. Ba za ku yi wani abu ba? Kada ku yi wata-wata, ku je kun mallaki ƙasar.
10 Cuando vayan allí, llegarán a un pueblo que vive sin pensar en el peligro; y la tierra es amplia, y Dios la ha entregado en sus manos: un lugar donde hay toda en la tierra para las necesidades del hombre.
Sa’ad da kun kai can, za ku iske mutanen suna zama a sake, ƙasar kuwa mai faɗi ce wadda Allah ya sa a hannuwanku, ƙasar da ba tă rasa kome ba.”
11 Entonces, seiscientos hombres de los danitas de Zora y Estaol salieron armados con instrumentos de guerra.
Sai mutane ɗari shida daga kabilar Dan suka yi ɗamarar yaƙi, suka tashi daga Zora da Eshtawol.
12 Y subieron y pusieron sus campamentos en Quiriat-jearim en Judá; por eso ese lugar se llama Mahane-dan hasta hoy. Está al oeste de Quiriat-jearim.
A kan hanyarsu suka kafa sansani kusa da Kiriyat Yeyarim a Yahuda. Shi ya sa a ana kira wurin nan yamma da Kiriyat Yeyarim Mahane Dan har wa yau.
13 De allí se dirigieron a la región montañosa de Efraín y llegaron a la casa de Micaías.
Daga can suka tafi ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika.
14 Entonces los cinco hombres que habían ido a hacer una búsqueda por el país de Lais dijeron a sus hermanos: ¿Saben que en estas casas hay un efod y dioses de la familia, una imagen tallada y una imagen de metal? Así que ahora considera qué hacer.
Sa’an nan mutum biyar ɗin nan da suka leƙi asirin ƙasar Layish suka ce wa’yan’uwansu, “Kun san cewa ɗaya daga cikin gidajen nan yana da efod, waɗansu allolin iyali, siffar da aka sassaƙa da kuma gunki na zubi? To, kun san abin da za ku yi.”
15 Y saliendo de su camino, vinieron a la casa del joven levita, la casa de Micaías, y le dijeron: ¿Te parece bien?
Saboda haka suka juya a wurin suka shiga gidan saurayin nan Balawe a wajen Mika suka gaishe shi.
16 Y los seiscientos hombres armados de los daneses tomaron sus lugares junto a la puerta.
Mutanen Dan ɗari shida da suka sha ɗamarar yaƙi suka tsaya a bakin ƙofa.
17 Luego, los cinco hombres que habían ido a hacer una búsqueda por la tierra, entraron y tomaron la imagen tallada y el efod y los dioses de la familia y la imagen fundida; y el sacerdote estaba junto a la puerta con los seiscientos hombres armados.
Sai mutum biyar da suka leƙi asirin ƙasar suka shiga ciki suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi yayinda firist ɗin tare da mutane ɗari shida da suka yi ɗamarar yaƙi suna tsaye a bakin ƙofa.
18 Y cuando entraron en la casa de Micaías y sacaron la imagen tallada y el efod y los dioses de la familia y la imagen fundida, el sacerdote les dijo: ¿Qué están haciendo?
Sa’ad da waɗannan mutane suka shiga gidan Mika suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi, sai firist ya ce musu, “Me kuke yi?”
19 Y ellos le dijeron: Cállate; no digas nada, ven con nosotros y sé nuestro padre y sacerdote; ¿Es mejor para ti ser sacerdote de la casa de un hombre o ser sacerdote de una tribu y una familia en Israel?
Suka ce, “Ka yi shiru! Kada ka ce wani abu. Zo tare da mu, ka zama mahaifinmu da kuma firist. Bai fi maka ka yi wa kabila da kuma zuriya a Isra’ila aikin firist ba, da ka bauta wa iyali guda kawai?”
20 Entonces se alegró el corazón del sacerdote, y tomó el efod y los dioses de la familia y la imagen tallada y se fue con la gente.
Sai firist ya yi farin ciki. Ya ɗauki efod, sauran allolin gida da siffar da aka sassaƙa ya tafi tare da mutanen.
21 Volvieron a emprender el camino y pusieron delante de ellos a los pequeños, a los bueyes y a los bienes.
Suka sa’ya’yansu ƙanana a gaba, dabbobinsu da mallakansu a gabansu, suka juya suka tafi.
22 Cuando se habían alejado de la casa de Micaías, los hombres de las casas cercanas a la casa de Miquea se reunieron y tomaron a los hijos de Dan.
Sa’ad da suka yi ɗan nisa daga gidan Mika, sai aka kira mutanen da suke maƙwabtakar da Mika suka taru suka bi mutanen Dan suka cim musu.
23 Gritándoles. Y los daneses, volviéndose, dijeron a Micaías: ¿Cuál es tu problema, que has tomado las armas?
Da suna ihu suna binsu, sai mutanen Dan suka waiga suka cewa Mika, “Mece ce damuwarka da ka kira mutanenka su zo su fāɗa mana?”
24 Y él dijo: Tú tomaste los dioses que yo hice, y mi sacerdote, y te fuiste; ¿Qué hay para mí ahora? ¿Por qué entonces me dices, ¿cuál es tu problema?
Ya amsa ya ce, “Kun kwashe allolin da na yi, da kuma firist nawa, kuka tafi. Me kuma nake da shi? Yaya za ku ce, ‘Mece ce damuwata?’”
25 Y los hijos de Dan le dijeron: No digas más, o uno de los nuestros se enfurezca y pueda atacarte, causando la pérdida de tu vida y la de tu gente.
Mutanen Dan suka ce, “Kada ka kuskura ka ce kome, in ba haka ba mutanen nan za su harzuƙa, da kai da iyalinka duka ku rasa rayukanku.”
26 Entonces los hijos de Dan siguieron su camino; y cuando Micaias vio que eran más fuertes que él, volvió a su casa.
Saboda haka mutanen Dan suka kama hanyarsu, Mika kuwa da ya ga an fi ƙarfinsa, sai ya juya ya koma gida.
27 Y ​​tomaron lo que Micaías había hecho, y su sacerdote, y fueron a Lais, a un pueblo que vivía en silencio y sin pensar en el peligro, y los metieron a la espada sin piedad, quemando su ciudad.
Sa’an nan suka ɗauko abin da Mika ya yi, da firist nasa, suka tafi Layish, suka fāɗa wa mutanen da suke zaman lafiya, ransu kuma a kwance. Suka fāɗa musu suka kuma ƙone birninsu.
28 Y no tenían salvador, porque estaba lejos de Sidón, y no tenían negocios con Aram; y estaba en el valle que es propiedad de Bet-rehob. Y reconstruyendo la ciudad, la tomaron para vivir.
Ba wanda zai cece su domin suna nesa da Bet-Sidon kuma ba sa hulɗa da kowa. Birnin yana a kwari kusa da Bet-Rekob. Mutanen Dan suka sāke gina birnin suka zauna a can.
29 Y le dieron a la ciudad el nombre de Dan, así como Dan su padre, que era hijo de Israel: aunque la ciudad había sido nombrada Lais al principio.
Suka sa wa birnin suna Dan, wato, sunan kakansu Dan, wanda aka haifa wa Isra’ila, ko da yake a dā ana kira birnin Layish.
30 Y los hijos de Dan levantaron para sí la imagen de talla; y Jonatán, el hijo de Gersón, el hijo de Moisés, y sus hijos, fueron sacerdotes de la tribu de los danitas, hasta el día en que el arca fue tomada prisionera.
A can mutanen Dan suka kafa wa kansu gumaka, Yonatan ɗan Gershom, ɗan Musa, da’ya’yansa maza firistoci ne na kabilar Dan har lokacin da aka kwashe mutane zuwa bauta.
31 Y tuvieron levantada la imagen de talla que Micaías había hecho, y fue allí todo el tiempo que la casa de Dios estuvo en Silo.
Suka ci gaba da amfani da gumakan da Mika ya yi, a duk wannan lokacin gidan Allah yana a Shilo.

< Jueces 18 >