< 1 Crónicas 29 >

1 Y el rey David dijo a todo el pueblo: Salomón, mi hijo, el único que ha sido escogido por Dios, todavía es joven y de tierna edad, y la obra es enorme, porque esta gran casa no es para el hombre, sino para el Señor Dios.
Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
2 Ahora, hasta donde puedo, he preparado lo que se necesita para la casa de mi Dios; el oro para las cosas de oro, y la plata para las cosas de plata, y el bronce para las cosas de bronce, hierro para las cosas de hierro, y madera para las cosas de madera; Berilos y joyas para enmarcar, y piedras de diferentes colores para adornos; todo tipo de piedras de gran precio y mármol en abundancia.
Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
3 Y como esta casa de Dios me es muy querida, le doy mi propiedad personal oro y plata a la casa de mi Dios, además de todo lo que tengo preparado para la casa sagrada;
Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
4 Incluso tres mil talentos de oro de Ofir y siete mil talentos de la mejor plata, para revestir las paredes de la casa:
talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
5 Oro para las cosas de oro, y plata para las cosas de plata, y para cada tipo de trabajo que deben realizar los expertos. ¿Quién entonces se presentará, ofreciéndose este día para la obra del Señor?
don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
6 Entonces los jefes de familia y los jefes de las tribus de Israel, y los capitanes de miles y cientos, con los controladores de los asuntos del rey, se entregaron libremente;
Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
7 Y dieron para el uso de la casa del Señor, cinco mil talentos y diez mil monedas de oro, y diez mil talentos de plata, y dieciocho mil talentos de bronce, y cien mil talentos de hierro.
Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
8 Y los que tenían piedras de gran precio las entregaron a la tienda de la casa del Señor, bajo el cuidado de Jehiel de Gersón.
Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
9 Entonces la gente se alegró porque sus ofrendas fueron dadas libremente, porque de todo corazón verdadero dieron libremente lo que tenían al Señor; y el rey David se llenó de alegría.
Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
10 Entonces, alabó David al Señor delante de todo el pueblo; Y David dijo: Alabado seas, oh Señor Dios de Israel, nuestro padre por los siglos de los siglos.
Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
11 Tuya, oh Señor, es la grandeza, el poder, la gloria, la autoridad, dominio, el honor: porque todo lo que está en los cielos y en la tierra es tuyo; tuyo es el reino, oh Señor, y tú eres superior a todos.
Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
12 La riqueza y el honor provienen de ti, y tú eres el gobernante de todo, y en tu mano hay poder y fortaleza; está en tu poder hacer grande y dar fuerza a todos.
Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
13 Ahora, Dios nuestro, te alabamos y honramos la gloria de tu nombre.
Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
14 ¿Pero quién soy yo y que es mi pueblo, para que tengamos el poder de dar libremente de esta manera? porque todas las cosas provienen de ti, y lo que te hemos dado es tuyo.
“Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
15 Porque nosotros, como todos nuestros padres, somos como hombres de un país extranjero delante de ti, que tenemos un lugar en la tierra por un tiempo; nuestros días en la tierra son como una sombra, y no hay esperanza de continuar.
Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
16 Oh Señor nuestro Dios, toda esta riqueza, que hemos preparado para la construcción de un templo para tu santo nombre, proviene de tu mano y es tuya.
Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
17 Y estoy consciente, Dios mío, de que tú examinas los corazones, y que te agrada la rectitud que te complaces en la justicia. En cuanto a mí, con un corazón recto, he dado libremente todas estas cosas; y he visto con alegría a tu gente que está aquí para hacer sus ofrendas libremente.
Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
18 Oh Señor, el Dios de Abraham, de Isaac y de Israel, nuestros padres, guarda esto para siempre en los pensamientos más profundos de tu pueblo, y deja que sus corazones sean fijos y fieles a ti;
Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
19 Y dale a Salomón, hijo mío, un corazón verdadero, para cumplir tus órdenes, tus reglas y tus leyes, y para hacer todas estas cosas, y para que pueda construir el templo para la cual he preparado.
Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
20 Y David dijo a todo el pueblo: Ahora alaba al Señor tu Dios. Y todo el pueblo alabó al Señor, el Dios de sus padres, con cabezas inclinadas que adoraban al Señor y al rey.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
21 E hicieron ofrendas al Señor, y ofrecieron holocaustos al Señor, al día siguiente, mil bueyes, mil ovejas y mil corderos, con sus ofrendas de bebida y una gran riqueza de ofrendas por todo Israel.
Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
22 Y con gran gozo hicieron una fiesta delante del Señor ese día. E hicieron rey a Salomón, el hijo de David, por segunda vez, le ungieron para santificarlo al Señor como gobernante, y a Sadoc como sacerdote.
Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
23 Así que Salomón fue puesto en el trono del Señor como rey en lugar de su padre David, y todo le fue bien; y todo Israel estaba bajo su autoridad.
Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
24 Y todos los jefes y los hombres de guerra y todos los hijos del rey David se pusieron bajo la autoridad del rey Salomón.
Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
25 Y él Señor hizo grande a Salomón ante los ojos de todo Israel, vistiéndolo con gloria y honor como ningún otro rey en Israel había tenido antes que él.
Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
26 Y David, hijo de Isaí, era rey sobre todo Israel.
Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
27 Durante cuarenta años reinó como rey sobre Israel, siete años en Hebrón y treinta y tres años en Jerusalén.
Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
28 Y llegó a su fin después de una larga vida, llena de días y gran riqueza y honor; y su hijo Salomón se hizo rey en su lugar.
Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
29 Ahora, todos los hechos de David, primero y último, están registrados en las palabras de Samuel el profeta, y las palabras de Natán el profeta, y las palabras de Gad el profeta;
Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
30 Junto con todo su gobierno y su poder, y los acontecimientos que tuvieron lugar en su tiempo, en Israel y en todos los reinos de otras tierras.
tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.

< 1 Crónicas 29 >