< Salmos 47 >

1 Al Vencedor: a los hijos de Coré: Salmo. Pueblos todos, batid las manos; aclamad a Dios con voz de júbilo.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 Porque el SEÑOR es Sublime y temible; Rey grande sobre toda la tierra.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 El guiará a los pueblos debajo de nosotros, y a los gentiles debajo de nuestros pies.
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 El nos elegirá nuestras heredades; la hermosura de Jacob, al cual amó. (Selah)
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 Subió Dios con júbilo, el SEÑOR con voz de trompeta.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 Cantad a Dios, cantad; cantad a nuestro Rey, cantad.
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 Porque el Rey de toda la tierra es Dios; cantad con entendimiento.
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 Reinó Dios sobre los gentiles; se sentó Dios sobre el trono de su santidad.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 Los príncipes de los pueblos se juntaron al pueblo del Dios de Abraham; porque de Dios son los escudos de la tierra; El es muy ensalzado.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.

< Salmos 47 >