< Salmos 89 >

1 Masquil de Ethán Ezrahita. LAS misericordias de Jehová cantaré perpetuamente: en generación y generación haré notoria tu verdad con mi boca.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Porque dije: Para siempre será edificada misericordia; en los mismos cielos apoyarás tu verdad.
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 Hice alianza con mi escogido; juré á David mi siervo, [diciendo]:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 Para siempre confirmaré tu simiente, y edificaré tu trono por todas las generaciones. (Selah)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Y celebrarán los cielos tu maravilla, oh Jehová; tu verdad también en la congregación de los santos.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Porque ¿quién en los cielos se igualará con Jehová? ¿quién será semejante á Jehová entre los hijos de los potentados?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 Dios terrible en la grande congregación de los santos, y formidable sobre todos cuantos están alrededor suyo.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 Oh Jehová, Dios de los ejércitos, ¿quién como tú? Poderoso eres, Jehová, y tu verdad está en torno de ti.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Tú tienes dominio sobre la bravura de la mar: cuando se levantan sus ondas, tú las sosiegas.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Tú quebrantaste á Rahab como á un muerto: con el brazo de tu fortaleza esparciste á tus enemigos.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Tuyos los cielos, tuya también la tierra: el mundo y su plenitud, tú lo fundaste.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Al aquilón y al austro tú los criaste: Tabor y Hermón cantarán en tu nombre.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Tuyo el brazo con valentía; fuerte es tu mano, ensalzada tu diestra.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Justicia y juicio son el asiento de tu trono: misericordia y verdad van delante de tu rostro.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Bienaventurado el pueblo que sabe aclamarte: andarán, oh Jehová, á la luz de tu rostro.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 En tu nombre se alegrarán todo el día; y en tu justicia serán ensalzados.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Porque tú eres la gloria de su fortaleza; y por tu buena voluntad ensalzarás nuestro cuerno.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Porque Jehová es nuestro escudo; y nuestro rey es el Santo de Israel.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Entonces hablaste en visión á tu santo, y dijiste: Yo he puesto el socorro sobre valiente; he ensalzado [un] escogido de mi pueblo.
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 Hallé á David mi siervo; ungílo con el aceite de mi santidad.
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 Mi mano será firme con él, mi brazo también lo fortificará.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 No lo avasallará enemigo, ni hijo de iniquidad lo quebrantará.
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 Mas yo quebrantaré delante de él á sus enemigos, y heriré á sus aborrecedores.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 Y mi verdad y mi misericordia serán con él; y en mi nombre será ensalzado su cuerno.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Asimismo pondré su mano en la mar, y en los ríos su diestra.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 El me llamará: Mi padre eres tú, mi Dios, y la roca de mi salud.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Yo también le pondré [por] primogénito, alto sobre los reyes de la tierra.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 Para siempre le conservaré mi misericordia; y mi alianza será firme con él.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 Y pondré su simiente para siempre, y su trono como los días de los cielos.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Si dejaren sus hijos mi ley, y no anduvieren en mis juicios;
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 Si profanaren mis estatutos, y no guardaren mis mandamientos;
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 Entonces visitaré con vara su rebelión, y con azotes sus iniquidades.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Mas no quitaré de él mi misericordia, ni falsearé mi verdad.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 No olvidaré mi pacto, ni mudaré lo que ha salido de mis labios.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 Una vez he jurado por mi santidad, que no mentiré á David.
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Su simiente será para siempre, y su trono como el sol delante de mí.
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Como la luna será firme para siempre, y [como] un testigo fiel en el cielo. (Selah)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Mas tú desechaste y menospreciaste á tu ungido; y te has airado [con él].
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Rompiste el pacto de tu siervo; has profanado su corona [hasta] la tierra.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Aportillaste todos sus vallados; has quebrantado sus fortalezas.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Menoscabáronle todos los que pasaron por el camino: es oprobio á sus vecinos.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Has ensalzado la diestra de sus enemigos; has alegrado á todos sus adversarios.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Embotaste asimismo el filo de su espada, y no lo levantaste en la batalla.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Hiciste cesar su brillo, y echaste su trono por tierra.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Has acortado los días de su juventud; hasle cubierto de afrenta. (Selah)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 ¿Hasta cuándo, oh Jehová? ¿te esconderás para siempre? ¿arderá tu ira como el fuego?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Acuérdate de cuán corto sea mi tiempo: ¿por qué habrás criado en vano á todos los hijos del hombre?
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 ¿Qué hombre vivirá y no verá muerte? ¿librarás su vida del poder del sepulcro? (Selah) (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Señor, ¿dónde están tus antiguas misericordias, que juraste á David por tu verdad?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Señor, acuérdate del oprobio de tus siervos; [oprobio que] llevo yo en mi seno de muchos pueblos.
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 Porque tus enemigos, oh Jehová, han deshonrado, porque tus enemigos han deshonrado los pasos de tu ungido.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Bendito Jehová para siempre. Amén, y Amén.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Salmos 89 >