< Proverbios 20 >

1 El vino hace burlador: la cerveza, alborotador; y cualquiera que en él errare, no será sabio.
Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
2 Bramido, como de cachorro de león, es el miedo del rey: el que le hace enojar, peca contra su alma.
Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
3 Honra es del hombre dejarse de pleito: mas todo insensato se envolverá en él.
Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
4 El perezoso no ara a causa del invierno: mas él pedirá en la segada, y no hallará.
Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
5 Aguas profundas es el consejo en el corazón del hombre: mas el hombre entendido le alcanzará.
Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
6 Muchos hombres pregonan cada cual el bien que han hecho: mas hombre de verdad ¿quién le hallará?
Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
7 El justo que camina en su integridad, bienaventurados serán sus hijos después de él.
Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
8 El rey que está en el trono de juicio, con su mirar disipa todo mal.
Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
9 ¿Quién podrá decir: Yo he limpiado mi corazón, limpio estoy de mi pecado?
Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
10 Doblada pesa, y doblada medida, abominación son a Jehová ambas cosas.
Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
11 El muchacho aun es conocido por sus obras, si su obra es limpia y recta.
Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
12 El oído oye, y el ojo ve: Jehová hizo aun ambas cosas.
Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
13 No ames el sueño, porque no te empobrezcas: abre tus ojos, hartarte has de pan.
Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
14 El que compra, dice: Malo es, malo es: mas en apartándose, él se alaba.
“Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
15 Hay oro, y multitud de piedras preciosas: mas los labios sabios son vaso precioso.
Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
16 Quítale su ropa, porque fió al extraño; y préndale por la extraña.
A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
17 Sabroso es al hombre el pan de mentira: mas después, su boca será llena de cascajo.
Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
18 Los pensamientos con el consejo se ordenan; y con industria se hace la guerra.
Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
19 El que descubre el secreto, anda en chismes; y con el que lisonjea de sus labios, no te entremetas.
Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
20 El que maldice a su padre, o a su madre, su candela será apagada en oscuridad tenebrosa.
In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
21 La herencia adquirida de priesa en el principio, su postrimería aun no será bendita.
Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
22 No digas: Yo me vengaré: espera a Jehová, y él te salvará.
Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
23 Abominación son a Jehová las pesas dobladas; y el peso falso, no es bueno.
Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
24 De Jehová son los pasos del hombre: el hombre pues, ¿cómo entenderá su camino?
Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
25 Lazo es al hombre tragar santidad; y después de los votos andar preguntando.
Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
26 El rey sabio esparce los impíos; y sobre ellos hace tornar la rueda.
Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
27 Candela de Jehová es el alma del hombre, que escudriña lo secreto del vientre.
Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
28 Misericordia y verdad guardan al rey; y con clemencia sustenta su trono.
Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
29 La honra de los mancebos es su fortaleza; y la hermosura de los viejos, su vejez.
Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
30 Las señales de las heridas son medicina en el malo; y las plagas en lo secreto del vientre.
Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.

< Proverbios 20 >