< San Mateo 22 >

1 Y respondiendo Jesús, les volvió a hablar en parábolas, diciendo:
Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace,
2 El reino de los cielos es semejante a un hombre rey, que hizo bodas a su hijo.
“Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure.
3 Y envió sus siervos para que llamasen a los convidados a las bodas; mas no quisieron venir.
Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.
4 Volvió a enviar otros siervos, diciendo: Decíd a los convidados: He aquí, mi comida he aparejado, mis toros y animales engordados son muertos, y todo está aparejado: veníd a las bodas.
Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, “Ku gaya wa wadanda aka gayyata, “Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren.”
5 Mas ellos no hicieron caso, y se fueron, uno a su labranza, y otro a sus negocios;
Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa.
6 Y otros, tomando sus siervos, afrentáronlos, y matáronlos.
Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su.
7 Y el rey, oyendo esto, se enojó; y enviando sus ejércitos, destruyó a aquellos homicidas, y puso a fuego su ciudad.
Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
8 Entonces dice a sus siervos: Las bodas a la verdad están aparejadas; mas los que eran llamados, no eran dignos.
Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba.
9 Id pues a las salidas de los caminos, y llamád a las bodas a cuantos hallareis.
Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.'
10 Y saliendo los siervos por los caminos, juntaron todos los que hallaron, juntamente malos y buenos; y las bodas fueron llenas de convidados.
Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
11 Y entró el rey para ver los convidados, y vio allí un hombre no vestido de vestido de boda.
Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba.
12 Y le díjo: Amigo, ¿cómo entraste acá no teniendo vestido de boda? Y a él se le cerró la boca.
Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
13 Entonces el rey dijo a los que servían: Atado de pies y de manos, tomádle, y echádle en las tinieblas de afuera: allí será el lloro, y el crujir de dientes.
Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.'
14 Porque muchos son llamados; mas pocos escogidos.
Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba.”'
15 Entonces idos los Fariseos, consultaron como le tomarían en alguna palabra.
Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa.
16 Y envían a él sus discípulos, con los de Heródes, diciendo: Maestro, sabemos que eres amador de verdad, y que enseñas con verdad el camino de Dios; y que no te cuidas de nadie; porque no tienes acepción de persona de hombres:
Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, “Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane.
17 Dinos pues, ¿qué te parece? ¿Es lícito dar tributo a César, o no?
To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?”
18 Mas Jesús, entendida su malicia, les dice: ¿Por qué me tentáis, hipócritas?
Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, “Don me kuke gwada ni, ku munafukai?
19 Mostrádme la moneda del tributo. Y ellos le presentaron un denario.
Ku nuna mani sulen harajin.” Sai suka kawo masa sulen.
20 Entonces les dice: ¿Cúya es esta figura, y lo que está encima escrito?
Yesu yace masu, “Hoto da sunan wanene wadannan?”
21 Ellos le dicen: De César. Y les dice: Pagád, pues, a César lo que es de César, y a Dios, lo que es de Dios.
Suka ce masa, “Na Kaisar.” Sai Yesu ya ce masu, “To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah.”
22 Y oyendo esto se maravillaron, y dejáronle, y se fueron.
Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
23 Aquel día llegaron a él los Saduceos, que dicen no haber resurrección, y le preguntaron,
A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi,
24 Diciendo: Maestro, Moisés dijo: Si alguno muriere sin hijos, su hermano se case con su mujer, y despertará simiente a su hermano.
cewa, “Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
25 Fueron, pues, entre nosotros siete hermanos; y el primero tomó mujer, y murió; y no teniendo generación, dejó su mujer a su hermano.
Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa.
26 De la misma manera también el segundo, y el tercero, hasta los siete.
Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai.
27 Y después de todos murió también la mujer.
Bayan dukansu, sai matar ta mutu.
28 En la resurrección, pues, ¿cúya de los siete será la mujer? porque todos la tuvieron.
To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta.”
29 Entonces respondiendo Jesús, les dijo: Erráis, ignorando las escrituras, y el poder de Dios.
Amma Yesu ya amsa yace masu, “Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba.
30 Porque en la resurrección, ni se casan, ni se dan en matrimonio; mas son como los ángeles de Dios en el cielo.
Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
31 Y de la resurrección de los muertos, ¿no habéis leído lo que es dicho por Dios a vosotros, que dice:
Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa,
32 Yo soy el Dios de Abraham, y el Dios de Isaac, y el Dios de Jacob? Dios no es Dios de los muertos, sino de los que viven.
'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu.”
33 Y oyendo esto las multitudes estaban fuera de sí de su doctrina.
Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
34 Entonces los Fariseos, oyendo que había cerrado la boca a los Saduceos, se juntaron a una;
Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu.
35 Y preguntó uno de ellos, intérprete de la ley, tentándole, y diciendo:
Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi-
36 Maestro, ¿cuál es el mandamiento grande en la ley?
“Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?”
37 Y Jesús le dijo: Amarás al Señor tu Dios de todo tu corazón, y de toda tu alma, y de toda tu mente.
Yesu yace masa, “Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.'
38 Este es el primero y el grande mandamiento.
Wannan itace babbar doka ta farko.
39 Y el segundo es semejante a éste: Amarás a tu prójimo como a ti mismo.
Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.'
40 De estos dos mandamientos depende toda la ley, y los profetas.
Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya.”
41 Y estando juntos los Fariseos, Jesús les preguntó,
Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya.
42 Diciendo: ¿Qué os parece del Cristo? ¿Cúyo hijo es? Dícenle ellos: De David.
Yace, “Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?” Suka ce masa, ''Dan Dauda ne.”
43 El les dice: Pues, ¿cómo David en Espíritu le llama Señor, diciendo:
Yesu yace masu, “To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa,
44 Dijo el Señor a mi Señor: Asiéntate a mi diestra, entre tanto que pongo tus enemigos por estrado de tus pies?
“Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka.”
45 Pues si David le llama Señor, ¿cómo es su hijo?
Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?”
46 Y nadie le podía responder palabra: ni osó alguno desde aquel día preguntarle más.
Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.

< San Mateo 22 >