< San Lucas 2 >

1 Y aconteció en aquellos días, que salió un edicto de parte de Augusto César, para que toda la tierra fuese empadronada.
Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
2 Este empadronamiento primero fue hecho, siendo presidente de la Siria Cirenio,
Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
3 E iban todos para ser empadronados cada uno a su ciudad.
Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
4 Y subió José de Galilea, de la ciudad de Nazaret, a Judea, a la ciudad de David, que se llama Belén, por cuanto era de la casa y familia de David;
Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
5 Para ser empadronado, con María su mujer desposada con él, la cual estaba preñada.
Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
6 Y aconteció, que estando ellos allí, los días en que ella había de parir se cumplieron.
Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
7 Y parió a su hijo primogénito, y le envolvió en pañales, y le acostó en el pesebre; porque no había lugar para ellos en el mesón.
Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
8 Y había pastores en la misma tierra, que velaban, y guardaban las velas de la noche sobre su ganado.
A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
9 Y, he aquí, el ángel del Señor vino sobre ellos; y la claridad de Dios los cercó de resplandor de todas partes, y tuvieron gran temor.
Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
10 Mas el ángel les dijo: No temáis, porque, he aquí, os doy nuevas de gran gozo, que será a todo el pueblo:
Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
11 Que os es nacido hoy Salvador, que es el Señor, el Cristo, en la ciudad de David.
Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
12 Y esto os será por señal: hallaréis al niño envuelto en pañales, echado en el pesebre.
Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
13 Y repentinamente apareció con el ángel multitud de ejércitos celestiales, que alababan a Dios, y decían:
Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
14 Gloria en las alturas a Dios, y en la tierra paz, y a los hombres buena voluntad.
“Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
15 Y aconteció, que como los ángeles se fueron de ellos al cielo, los pastores dijeron los unos a los otros: Pasemos, pues, hasta Belén, y veamos este negocio que ha hecho Dios, y nos ha mostrado.
Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
16 Y vinieron a priesa, y hallaron a María, y a José, y al niño acostado en el pesebre.
Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
17 Y viéndo lo, hicieron notorio lo que les había sido dicho del niño.
Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
18 Y todos los que lo oyeron, se maravillaron de lo que los pastores les decían.
Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
19 Mas María guardaba todas estas cosas confiriéndo las en su corazón.
Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
20 Y se volvieron los pastores glorificando y alabando a Dios por todas las cosas que habían oído y visto, como les había sido dicho.
Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
21 Y pasados los ocho días para circuncidar al niño, llamaron su nombre Jesús, el cual fue así llamado por el ángel antes que él fuese concebido en el vientre.
Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
22 Y como se cumplieron los días de la purificación de María conforme a la ley de Moisés, le trajeron a Jerusalem para presentar le al Señor,
Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
23 (Como está escrito en la ley del Señor: Todo varón que abriere la matriz, será llamado santo al Señor; )
Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
24 Y para dar la ofrenda, conforme a lo que está dicho en la ley del Señor, un par de tórtolas, o dos palominos.
Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
25 Y, he aquí, había un hombre en Jerusalem llamado Simeón, y este hombre, justo y piadoso, esperaba la consolación de Israel; y el Espíritu Santo era sobre él.
Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
26 Y había recibido respuesta del Espíritu Santo, que no vería la muerte antes que viese al Cristo del Señor.
An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
27 Y vino por el Espíritu al templo. Y como metieron al niño Jesús sus padres en el templo, para hacer por él conforme a la costumbre de la ley,
Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
28 Entonces él le tomó en sus brazos, y bendijo a Dios, y dijo:
sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
29 Ahora despides, Señor, a tu siervo, conforme a tu palabra, en paz:
“Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
30 Porque han visto mis ojos tu salud,
Domin idanuna sun ga cetonka,
31 La cual has aparejado en presencia de todos los pueblos:
wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
32 Luz para ser revelada a los Gentiles, y la gloria de tu pueblo Israel.
Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
33 Y José y su madre estaban maravillados de las cosas que se decían de él.
Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
34 Y los bendijo Simeón, y dijo a su madre María: He aquí, que este niño es puesto para caída y para levantamiento de muchos en Israel, y para blanco de contradicción;
Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
35 (Y a tu alma de ti misma traspasará espada, ) para que de muchos corazones sean manifestados los pensamientos.
Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
36 Estaba también allí Ana, profetisa, hija de Fanuel, de la tribu de Aser, la cual era ya de grande edad, y había vivido con su marido siete años desde su virginidad.
Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
37 Y era viuda de hasta ochenta y cuatro años, que no se apartaba del templo, en ayunos y oraciones sirviendo a Dios de noche y de día.
sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
38 Y esta sobreviniendo en la misma hora, juntamente daba alabanzas al Señor, y hablaba de él a todos los que esperaban la redención en Jerusalem.
A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
39 Mas como cumplieron todas las cosas según la ley del Señor, se volvieron a Galilea, a su ciudad de Nazaret.
Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
40 Y el niño crecía, y era confortado en espíritu, y henchíase de sabiduría; y la gracia de Dios era sobre él.
Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
41 E iban sus padres todos los años a Jerusalem en la fiesta de la pascua.
Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
42 Y como fue de doce años, ellos subieron a Jerusalem conforme a la costumbre de la fiesta.
Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
43 Y acabados los días, volviendo ellos, se quedó el niño Jesús en Jerusalem, sin saber lo José y su madre.
Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
44 Y pensando que estaba en la compañía, anduvieron camino de un día; y le buscaban entre los parientes, y entre los conocidos.
Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
45 Y como no le hallasen, volvieron a Jerusalem, buscándole.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
46 Y aconteció, que tres días después le hallaron en el templo, sentado en medio de los doctores, oyéndoles, y preguntándoles.
Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
47 Y todos los que le oían, estaban fuera de sí por su entendimiento y respuestas.
Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
48 Y como le vieron, se espantaron; y le dijo su madre: Hijo, ¿por qué nos has hecho así? He aquí, tu padre y yo te hemos buscado con dolor.
Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
49 Entonces él les dice: ¿Qué hay? ¿por qué me buscabais? ¿No sabíais que en los negocios que son de mi Padre me conviene estar?
Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 Mas ellos no entendieron las palabras que les habló.
Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
51 Y descendió con ellos, y vino a Nazaret, y estaba sujeto a ellos. Y su madre guardaba todas estas cosas en su corazón.
Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
52 Y Jesús crecía en sabiduría, y en estatura, y en favor acerca de Dios y de los hombres.
Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.

< San Lucas 2 >