< Juan 10 >

1 De cierto, de cierto os digo, que el que no entra por la puerta en el aprisco de las ovejas, mas sube por otra parte, el tal ladrón es y robador.
“Hakika, Hakika, ina ce maku, wanda bai shiga ta kofa zuwa garken tumaki ba, amma ya haura ta wata hanya, wannan mutum barawo ne da dan fashi.
2 Mas el que entra por la puerta, el pastor de las ovejas es.
Wanda ya shiga ta kofa shine makiyayin tumakin.
3 A éste abre el portero, y las ovejas oyen su voz; y a sus ovejas llama por nombre, y las saca.
Mai gadin kofar zai bude masa. Tumakin suna jin muryarsa, ya na kuma kiran tumakinsa da sunayensu, ya kuma kai su waje.
4 Y como ha sacado fuera sus ovejas, va delante de ellas; y las ovejas le siguen; porque conocen su voz.
Bayanda ya kawo su duka a waje, yana tafiya a gabansu, sai tumakin su bi shi, domin sun san muryarsa.
5 Mas al extraño no seguirán, antes huirán de él; porque no conocen la voz de los extraños.
Ba za su bi bako ba amma sai dai su guje shi, domin basu san muryar baki ba.”
6 Esta parábola les dijo Jesús; mas ellos no entendieron qué era lo que les decía.
Yesu ya yi masu magana da wannan misali, amma basu gane wadannan abubuwa da yake gaya masu ba.
7 Volvióles pues Jesús a decir: De cierto, de cierto os digo, que yo soy la puerta de las ovejas.
Sai Yesu ya ce masu kuma, “Hakika, Hakika, Ina ce maku, Ni ne kofar tumaki.
8 Todos los que antes de mí vinieron, ladrones son y robadores, mas no los oyeron las ovejas.
Dukan wadanda suka zo kamin ni barayi ne da yan fashi, amma tumakin ba su ji su ba.
9 Yo soy la puerta: el que por mí entrare, será salvo; y entrará, y saldrá, y hallará pastos.
Ni ne kofa, In kowa ya shiga ta wurina, zai sami ceto, zai shiga ya fita ya kuma sami wurin kiwo.
10 El ladrón no viene sino para hurtar, y matar, y destruir: yo he venido para que tengan vida, y para que la tengan en grande abundancia.
Barawo ba ya zuwa sai don ya yi sata, ya kashe, ya kuma hallakar. Na zo ne domin su sami rai su kuma same shi a yalwace.
11 Yo soy el buen pastor: el buen pastor su alma da por las ovejas.
Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yana bada ransa domin tumakinsa.
12 Mas el asalariado, y que no es el pastor, cuyas no son proprias las ovejas, ve al lobo que viene, y deja las ovejas, y huye; y el lobo arrebata, y dispersa las ovejas.
Wanda yake dan sako kuma, ba makiyayi ba, wanda ba shine mai tumakin ba, in ya ga kyarkeci na zuwa sai ya saki tumakin ya gudu. Sai kyarkecin ya dauke su ya kuma warwatsa su.
13 Así que el asalariado huye, porque es asalariado, y no tiene cuidado de las ovejas.
Ya gudu domin shi mai aikin kudi ne kuma bai damu da tumakin ba.
14 Yo soy el buen pastor; y conozco mis ovejas, y las mías me conocen,
Nine makiyayi mai kyau, na kuma san nawa, nawa kuma sun san ni.
15 Como el Padre me conoce a mí, y yo conozco al Padre; y pongo mi vida por las ovejas.
Uban ya san ni, ni ma na san Uban, na kuma bada raina domin tumakin.
16 También tengo otras ovejas que no son de este redil: aquellas también he de traer, y oirán mi voz; y habrá un rebaño, y un pastor.
Ina da wadansu tumaki wadanda ba na wannan garken ba. Wadannan, kuma, dole in kawo su, su ma za su ji muryata saboda za su zama garke daya da makiyayi daya.
17 Por eso me ama el Padre, porque yo pongo mi vida, para volverla a tomar.
Domin wannan ne Uban yake kauna ta: Na bada raina domin in same shi kuma.
18 Nadie la quita de mí, mas yo la pongo de mí mismo; porque tengo poder para ponerla, y tengo poder para volverla a tomar. Este mandamiento recibí de mi Padre.
Babu wanda zai dauke shi daga wurina, amma ina bayar da shi da kaina. Ina da ikon bada shi, ina da iko in dauke shi kuma. Na karbi wannan umarnin daga wurin Ubana.”
19 Y volvió a haber disensión entre los Judíos por estas palabras.
Tsattsaguwa ta sake tashi tsakanin Yahudawa domin wadannan kalmomin.
20 Y muchos de ellos decían: Demonio tiene, y está loco: ¿para qué le oís?
Dayawa a cikinsu suka ce, yana da aljani, kuma mahaukaci ne. Don me ku ke sauraronsa?”
21 Decían otros: Estas palabras no son de endemoniado: ¿puede el demonio abrir los ojos de los ciegos?
Wadansu suka ce, wadannan ba kalmomin wanda yake da aljani ba ne. Ko mai aljani zai iya bude idanun makaho?”
22 Y hacíase la fiesta de la dedicación en Jerusalem, y era invierno.
Sai lokacin idin Tsarkakewa a Urushalima ya zo.
23 Y Jesús andaba en el templo por el pórtico de Salomón.
A lokacin damuna ne, Yesu kuwa yana tafiya a shirayi cikin haikalin Sulaimanu.
24 Y rodeáronle los Judíos, y le dijeron: ¿Hasta cuándo traes suspensa nuestra alma? Si tú eres el Cristo, dínoslo abiertamente.
Sai Yahudawa suka zagaye shi suka ce masa, “Har yaushe ne za ka bar mu cikin shakka? In kai ne Almasihun, ka gaya mana dalla-dalla.”
25 Respondióles Jesús: Os lo he dicho, y no lo creísteis: las obras que yo hago en nombre de mi Padre, estas dan testimonio de mí.
Yesu ya ce masu, “Na gaya maku, amma baku gaskata ba. Ayyukan da nake yi a cikin sunan Ubana, su ke yin shaida a kaina.
26 Mas vosotros no creéis, porque no sois de mis ovejas, como os he dicho.
Duk da haka baku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27 Mis ovejas oyen mi voz, y yo las conozco, y ellas me siguen;
Tumakina suna jin murya ta; Na san su, suna kuma bi na.
28 Y yo les doy vida eterna, y para siempre no perecerán, y nadie las arrebatará de mi mano. (aiōn g165, aiōnios g166)
Ina ba su rai na har abada; ba za su taba mutuwa ba, babu wanda zai kwace su daga hannu na. (aiōn g165, aiōnios g166)
29 Mi Padre que me las dio, mayor que todos es; y nadie las puede arrebatar de la mano de mi Padre.
Ubana, wanda ya bani su, ya fi kowa girma, kuma ba mai iya kwace su daga hannun Uban.
30 Yo y mi Padre somos uno.
Ni da Uban daya ne.”
31 Entonces volvieron a tomar piedras los Judíos, para apedrearle.
Sai Yahudawa suka dauki duwatsu kuma domin su jajjefe shi.
32 Respondióles Jesús: Muchas buenas obras os he mostrado de mi Padre, ¿por cuál obra de ellas me apedreáis?
Yesu ya amsa masu, “Na nuna maku kyawawan ayyuka masu yawa daga wurin Uban. Saboda wane daga cikin wadannan ayyukan kuke jefe ni?”
33 Respondiéronle los Judíos, diciendo: Por la buena obra no te apedreamos, sino por la blasfemia; y porque tú, siendo hombre, te haces Dios.
Sai Yahudawa suka amsa masa, “ba don wani aiki mai kyau muke son mu jefe ka ba, amma don sabo, domin kai, mutum ne, amma kana mayar da kanka Allah.”
34 Respondióles Jesús: ¿No está escrito en vuestra ley: Yo dije: Dioses sois?
Yesu ya amsa masu, “Ba a rubuce yake a shari'arku ba, 'Na ce, “ku alloli ne”'?”
35 Si llamó dioses a aquellos, a los cuales vino la palabra de Dios, y la Escritura no puede ser quebrantada,
In ya kira su alloli, su wadanda maganar Allah ta zo gare su (kuma ba za a iya karya nassi ba),
36 ¿A mí que el Padre santificó, y envió al mundo, vosotros decís: Tú blasfemas; porque dije: Soy el Hijo de Dios?
kuna gaya wa wanda Uban ya kebe ya kuma aiko cikin duniya, 'Kana sabo', domin Na ce, 'Ni dan Allah ne'?
37 Si no hago obras de mi Padre, no me creáis.
In ba na aikin Ubana, kada ku gaskata ni.
38 Mas si las hago, aunque a mí no creáis, creéd a las obras, para que conozcáis y creáis, que el Padre es en mí, y yo en él.
Amma, idan ina yin su, ko ba ku gaskata da ni ba, ku gaskata da ayyukan saboda ku sani, ku kuma gane cewa Uban yana ciki na, ni kuma ina cikin Uban.”
39 Y procuraban otra vez prenderle; mas él se salió de sus manos,
Suka sake kokarin kama shi, amma ya yi tafiyarsa, ya fita daga hannunsu.
40 Y volvióse tras el Jordán, a aquel lugar donde primero había estado bautizando Juan, y se estuvo allí.
Ya yi tafiyarsa kuma har gaba da kogin Urdun zuwa inda Yahaya ke yin baftisma ada, ya kuma zauna a wurin.
41 Y muchos venían a él, y decían: Juan a la verdad ningún milagro hizo; mas todo lo que Juan dijo de éste, era verdad.
Mutane masu yawa suka zo wurinsa, suka ce,”Hakika Yahaya bai yi wasu alamu ba, amma dukan abubuwan da Yahaya ya ce game da wannan mutum gaskiya ne.”
42 Y muchos creyeron allí en él.
Mutane dayawa suka bada gaskiya gare shi a wurin.

< Juan 10 >