< Job 40 >

1 Y respondió Jehová a Job, y dijo:
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 ¿Es sabiduría contender con el Omnipotente? El que disputa con Dios, responda a esto.
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 Y respondió Job a Jehová, y dijo:
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 He aquí, que yo soy vil, ¿qué te responderé? Mi mano pongo sobre mi boca.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 Una vez hablé, y no responderé; y dos veces; mas no tornaré a hablar.
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 Y respondió Jehová a Job desde la oscuridad, y dijo:
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 Cíñete ahora, como varón, tus lomos: yo te preguntaré, y házme saber.
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 ¿Invalidarás tú también mi juicio? ¿condenarme has a mi para justificarte a ti?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 ¿Tienes tú brazo como Dios? ¿y tronarás tú con voz como él?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Ahora atavíate de magestad y de alteza, y vístete de honra y de hermosura.
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Esparce furores de tu ira, y mira a todo soberbio, y abátele.
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 Mira a todo soberbio, y póstrale; y quebranta los impíos en su asiento.
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Encúbrelos a todos en el polvo; y ata sus rostros en oscuridad;
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 Y yo también te confesaré, que tu diestra te salvará.
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 He aquí ahora Behemot, al cual yo hice contigo; yerba come como buey.
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 He aquí ahora que su fuerza está en sus lomos; y su fortaleza en el ombligo de su vientre:
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 Su cola mueve como un cedro; y los nervios de sus genitales son entretejidos:
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 Sus huesos son fuertes como acero, y sus miembros como barras de hierro:
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 Él es la cabeza de los caminos de Dios: el que le hizo le acercará de su espada.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 Ciertamente los montes llevan renuevo para él; y toda bestia del campo retoza allá.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 Debajo de las sombras se echará, en lo oculto de las cañas, y de los lugares húmedos.
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Los árboles sombríos le cubren con su sombra; los sauces del arroyo le cercan.
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 He aquí que él robará el río que no corra; y confíase que el Jordán pasará por su boca.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 El le tomará por sus ojos en los tropezaderos, y le horadará la nariz.
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?

< Job 40 >