< Job 23 >

1 Y respondió Job, y dijo:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Hoy también hablaré con amargura, y será más grave mi llaga que mi gemido.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3 ¡Quién diese que le conociese, y le hallase! yo iría hasta su trono.
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4 Ordenaría juicio delante de él, y mi boca henchiría de argumentos.
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5 Yo sabría lo que él me respondería, y entendería lo que me dijese.
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6 ¿Pleitearía conmigo con multitud de fuerza? No: antes él la pondría en mí.
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7 Allí el recto disputaría con él; y escaparía para siempre de él que me condena.
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
8 He aquí, yo iré al oriente, y no le hallaré, y al occidente, y no le entenderé.
“Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
9 Si al norte él obrare, yo no le veré: al mediodía se esconderá, y no le veré.
Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
10 Mas él conoció mi camino: probóme, y salí como oro.
Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
11 Mis pies tomaron su rastro: guardé su camino, y no me aparté.
Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
12 Del mandamiento de sus labios nunca me quité: las palabras de su boca guardé más que mi comida.
Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
13 Y si él se determina en una cosa, ¿quién le apartará? Su alma deseó, e hizo.
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14 Por tanto él acabará lo que ha determinado de mí; y muchas cosas como estas hay en él.
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15 Por lo cual yo me espantaré delante de su rostro: consideraré, y temerle he.
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16 Dios ha enternecido mi corazón, y el Omnipotente me ha espantado.
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17 ¿Por qué yo no fui cortado delante de las tinieblas, y cubrió con oscuridad mi rostro?
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.

< Job 23 >