< San Lucas 1 >

1 Puesto que muchos han emprendido la tarea de poner en orden una narración relativa a los asuntos que se han cumplido entre nosotros,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 tal como nos lo transmitieron los que desde el principio fueron testigos oculares y servidores de la palabra,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 también me pareció bien, habiendo entendido el curso de todas las cosas con exactitud desde el principio, escribirte en orden, excelentísimo Teófilo;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 para que conozcas la certeza relativa a las cosas en las que fuiste instruido.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Había en los días de Herodes, rey de Judea, un sacerdote llamado Zacarías, de la división sacerdotal de Abías. Tenía una esposa de las hijas de Aarón, que se llamaba Elisabet.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ambos eran justos ante Dios, y andaban irreprochablemente en todos los mandamientos y ordenanzas del Señor.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Pero no tuvieron hijos, porque Elisabet era estéril, y ambos eran de edad avanzada.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Mientras ejercía el oficio sacerdotal ante Dios en el orden de su división
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 según la costumbre del oficio sacerdotal, le tocaba entrar en el templo del Señor y quemar incienso.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Toda la multitud del pueblo oraba fuera a la hora del incienso.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Se le apareció un ángel del Señor, de pie a la derecha del altar del incienso.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zacarías se turbó al verlo y le entró miedo.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Pero el ángel le dijo: “No temas, Zacarías, porque tu petición ha sido escuchada. Tu mujer, Elisabet, te dará a luz un hijo, y le pondrás por nombre Juan.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Tendrás alegría y gozo, y muchos se alegrarán de su nacimiento.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Porque será grande a los ojos del Señor, y no beberá vino ni bebida fuerte. Estará lleno del Espíritu Santo, incluso desde el vientre de su madre.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Hará que muchos de los hijos de Israel se conviertan al Señor, su Dios.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Irá delante de él con el espíritu y el poder de Elías, ‘para hacer volver el corazón de los padres a los hijos’, y a los desobedientes a la sabiduría de los justos; para preparar un pueblo preparado para el Señor.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zacarías dijo al ángel: “¿Cómo puedo estar seguro de esto? Porque soy un anciano, y mi mujer está muy avanzada en años”.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 El ángel le respondió: “Soy Gabriel, que está en la presencia de Dios. He sido enviado para hablarte y traerte esta buena noticia.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 He aquí que te quedarás callado y no podrás hablar hasta el día en que sucedan estas cosas, porque no creíste en mis palabras, que se cumplirán a su debido tiempo.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 La gente esperaba a Zacarías y se maravillaba de que se demorara en el templo.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Cuando salió, no pudo hablarles. Se dieron cuenta de que había tenido una visión en el templo. Siguió haciéndoles señales, y permaneció mudo.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Cuando se cumplieron los días de su servicio, se fue a su casa.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Después de estos días, concibió Elisabet, su mujer, y se escondió cinco meses, diciendo:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “Así me ha hecho el Señor en los días en que me ha mirado, para quitar mi oprobio entre los hombres.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 En el sexto mes, el ángel Gabriel fue enviado por Dios a una ciudad de Galilea llamada Nazaret,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 a una virgen comprometida a casarse con un hombre que se llamaba José, de la casa de David. La virgen se llamaba María.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Al entrar, el ángel le dijo: “¡Alégrate, muy favorecida! El Señor está contigo. Bendita eres entre las mujeres”.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Pero cuando lo vio, se preocupó mucho por el dicho, y pensó qué clase de saludo sería éste.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 El ángel le dijo: “No temas, María, porque has encontrado el favor de Dios.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 He aquí que concebirás en tu seno y darás a luz un hijo, al que pondrás por nombre “Jesús”.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Será grande y se llamará Hijo del Altísimo. El Señor Dios le dará el trono de su padre David,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 y reinará sobre la casa de Jacob para siempre. Su Reino no tendrá fin”. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 María dijo al ángel: “¿Cómo puede ser esto, siendo yo virgen?”.
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 El ángel le respondió: “El Espíritu Santo vendrá sobre ti, y el poder del Altísimo te cubrirá con su sombra. Por eso también el santo que nazca de ti será llamado Hijo de Dios.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 He aquí que también Elisabet, tu pariente, ha concebido un hijo en su vejez; y éste es el sexto mes de la que se llamaba estéril.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Porque nada de lo dicho por Dios es imposible.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 María dijo: “He aquí la sierva del Señor; hágase en mí según tu palabra”. Entonces el ángel se alejó de ella.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 En aquellos días, María se levantó y se fue de prisa a la región montañosa, a una ciudad de Judá,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 entró en casa de Zacarías y saludó a Isabel.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Cuando Isabel oyó el saludo de María, el niño saltó en su seno; e Isabel quedó llena del Espíritu Santo.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Gritó en voz alta y dijo: “Bendita eres entre las mujeres y bendito es el fruto de tu vientre.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 ¿Por qué soy tan favorecida, para que la madre de mi Señor venga a mí?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Porque cuando la voz de tu saludo llegó a mis oídos, el niño saltó de alegría en mi vientre.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 ¡Bienaventurada la que ha creído, porque se cumplirán las cosas que se le han dicho de parte del Señor!”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 María dijo, “Mi alma engrandece al Señor.
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Mi espíritu se ha alegrado en Dios, mi Salvador,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 pues ha mirado el humilde estado de su sierva. Porque he aquí que, a partir de ahora, todas las generaciones me llamarán dichosa.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Porque el que es poderoso ha hecho grandes cosas por mí. Santo es su nombre.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Su misericordia es por generaciones y generaciones sobre los que le temen.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Ha demostrado poder con su brazo. Ha dispersado a los orgullosos en la imaginación de sus corazones.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Ha derribado a los príncipes de sus tronos, y ha exaltado a los humildes.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Ha colmado de bienes a los hambrientos. Ha enviado a los ricos con las manos vacías.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Ha dado ayuda a Israel, su siervo, para que se acuerde de la misericordia,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 como habló con nuestros padres, a Abraham y a su descendencia para siempre”. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 María se quedó con ella unos tres meses y luego volvió a su casa.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Se cumplió el tiempo en que Elisabet debía dar a luz, y dio a luz un hijo.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Sus vecinos y sus parientes oyeron que el Señor había engrandecido su misericordia con ella, y se alegraron con ella.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Al octavo día vinieron a circuncidar al niño, y quisieron llamarlo Zacarías, como el nombre de su padre.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Su madre respondió: “No, sino que se llamará Juan”.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Le dijeron: “No hay nadie entre tus parientes que se llame así”.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Hicieron señas a su padre de cómo quería que se llamara.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Pidió una tablilla y escribió: “Se llama Juan”. Todos se maravillaron.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Al instante se le abrió la boca y se le liberó la lengua, y habló bendiciendo a Dios.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 El temor se apoderó de todos los que vivían alrededor, y todos estos dichos fueron comentados en toda la región montañosa de Judea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Todos los que los oían los guardaban en su corazón, diciendo: “¿Qué será entonces este niño?” La mano del Señor estaba con él.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Su padre Zacarías fue lleno del Espíritu Santo y profetizó diciendo,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Bendito sea el Señor, el Dios de Israel, porque ha visitado y redimido a su pueblo;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 y nos ha levantado un cuerno de salvación en la casa de su siervo David
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (como habló por boca de sus santos profetas que han sido desde la antigüedad), (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvación de nuestros enemigos y de la mano de todos los que nos odian;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 para mostrar misericordia hacia nuestros padres, para recordar su santa alianza,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 el juramento que hizo a Abraham, nuestro padre,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 que nos conceda que, siendo liberados de la mano de nuestros enemigos, debe servirle sin miedo,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 en santidad y justicia ante él todos los días de nuestra vida.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Y tú, niño, serás llamado profeta del Altísimo; porque irás delante de la cara del Señor para preparar sus caminos,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 para dar conocimiento de la salvación a su pueblo por la remisión de sus pecados,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 por la tierna misericordia de nuestro Dios, por la que nos visitará la aurora de lo alto,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 para iluminar a los que están en las tinieblas y en la sombra de la muerte; para guiar nuestros pies por el camino de la paz”.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 El niño crecía y se fortalecía en espíritu, y estuvo en el desierto hasta el día de su aparición pública ante Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< San Lucas 1 >