< 1 Crónicas 11 >

1 Entonces todos los israelitas se reunieron con David en Hebrón. Y le dijeron: “Somos tu carne y tu sangre.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 En los últimos tiempos, aunque Saúl era el rey, tú eras el verdadero líder de Israel. El Señor, tu Dios, te ha dicho: ‘Tú serás el pastor de mi pueblo, y tú serás el jefe de mi pueblo Israel’”.
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 Todos los ancianos de Israel acudieron ante el rey en Hebrón, y David hizo un acuerdo solemne con ellos ante el Señor. Allí ungieron a David como rey de Israel, tal como el Señor lo había prometido por medio de Samuel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 Entonces David y todos los israelitas fueron a Jerusalén (antes conocida como Jebús), donde vivían los jebuseos.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 Pero los jebuseos le dijeron a David: “No entrarás aquí”. Sin embargo, David capturó la fortaleza de Sión, ahora conocida como la Ciudad de David.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 Y David había dicho: “El primero que ataque a los jebuseos será mi comandante en jefe”. Como Joab, hijo de Sarvia, fue el primero, se convirtió en el comandante en jefe.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 David decidió habitar en la fortaleza, por eso la llamaron Ciudad de David.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 Entonces construyó la ciudad a su alrededor, desde el Milo e hizo un circuito alrededor, mientras que Joab reparaba el resto de la ciudad.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 David se hizo cada vez más poderoso, porque el Señor Todopoderoso estaba con él.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 Estos fueron los líderes de los poderosos guerreros de David que, junto con todos los israelitas, le dieron un fuerte apoyo para que se convirtiera en rey, tal como el Señor había prometido que sucedería con Israel.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 Esta es la lista de los principales guerreros que apoyaron a David: Jasobeam, hijo de Hacmoni, líder de los Tres. Con su lanza, una vez mató a 300 hombres en una sola batalla.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 Después de él vino Eleazar, hijo de Dodo, descendiente de Ahoha, uno de los Tres guerreros principales.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 Estaba con David en Pasdamin cuando los filisteos se reunieron para la batalla que tuvo lugar en un campo de cebada. El ejército israelita huyó cuando los filisteos atacaron,
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 pero David y Eleazar se apostaron en medio del campo, defendiendo su terreno y matando a los filisteos. El Señor los salvó dándoles una gran victoria.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 En otra ocasión, los Tres, que formaban parte de los Treinta guerreros principales, bajaron a recibir a David cuando estaba en la cueva de Adulam. El ejército filisteo estaba acampado en el valle de Refaim.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 En ese momento David estaba en la fortaleza, y la guarnición filistea estaba en Belén.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 David tenía mucha sed y dijo: “¡Ojalá alguien pudiera traerme un trago de agua del pozo que está junto a la puerta de la entrada de Belén!”
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 Los Tres atravesaron las defensas filisteas, tomaron un poco de agua del pozo de la puerta de Belén y se la llevaron a David. Pero David se negó a beberla y la vertió como ofrenda al Señor.
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 “¡Dios me libre de hacer esto!”, dijo. “Sería como beber la sangre de esos hombres que arriesgaron sus vidas. Ellos arriesgaron sus vidas para traerme una bebida”. Así que no la bebió. Estas son algunas de las cosas que hicieron los tres guerreros principales.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 Abisai, hermano de Joab, era el líder de los segundos Tres. Usando su lanza, una vez mató a 300 hombres, y se hizo famoso entre los Tres.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 Era el más apreciado de los Tres y era su comandante, aunque no fue uno de los primeros Tres.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Benaía, hijo de Joiada, un fuerte guerrero de Cabseel, hizo muchas cosas sorprendentes. Mató a dos hijos de Ariel de Moab. También fue tras un león a un pozo en la nieve y lo mató.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 En otra ocasión mató a un egipcio, un hombre enorme que medía dos metros y medio. El egipcio tenía una lanza cuyo asta era tan gruesa como la vara de un tejedor. Benaía lo atacó sólo con un garrote, pero pudo agarrar la lanza de la mano del egipcio, y lo mató con su propia lanza.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 Este fue el tipo de cosas que hizo Benaía y que lo hicieron tan famoso como los tres guerreros principales.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 Era el más apreciado de los Treinta, aunque no era uno de los Tres. David lo puso a cargo de su guardia personal.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 Otros guerreros principales eran: Asael, hermano de Joab; Elhanán, hijo de Dodo, de Belén;
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Sama el harodita; Heles el pelonita;
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Ira, hijo de Iques, de Tecoa; Abiezer, de Anatot;
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sibecai el husatita; Ilai el ahohita;
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharai, de Netofa; Heled, hijo de Baana, de Netofa;
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Itai, hijo de Ribai, de Guibeá, de los benjamitas; Benaía el Piratonita;
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Hurai de los valles de Gaas; Abiel de Arabá;
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Azmavet de Bahurim; Eliaba el Saalbonita;
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 Los hijos de Jasén el Gizonita; Jonatán, hijo de Sage el Ararita;
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Ahíam, hijo de Sacar el Ararita; Elifal, hijo de Ur;
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Hefer de Mequer; Ahías el pelonita;
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hezro el Carmelita; Naarai, hijo de Ezbai;
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Joel, hermano de Natán; Mibhar, hijo de Hagri;
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Zelek, el amonita; Naharai, de Beerot; el escudero de Joab, hijo de Sarvia;
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Ira, de Jatir; Gareb, de Jatir;
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Urías, el hitita; Zabad, hijo de Ahlai;
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Adina, hijo de Siza, rubenita, jefe de los rubenitas, y los treinta que estaban con él;
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanán, hijo de Maaca; Josafat mitnita;
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Uzías de Astarot; Sama y Jeiel, los hijos de Hotam de Aroer;
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Jediael, hijo de Simri, y su hermano, Joha el tizita;
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliel de Mahava; Jerebai y Josavía, los hijos de Elnaam; Itma el moabita;
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliel; Obed y Jaasiel, todos ellos de Soba.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.

< 1 Crónicas 11 >