< Luka 5 >

1 Busuba nabumbi Yesu walikuba wemana mumbali mwa lwenje lwa Genesaleti. Bantu bangi bali kabanyakana kwambeti banyumfwe Maswi a Lesa.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Lino Yesu walabona mato abili asungwa mumbali, beshikushina inswi balikuba balafumumo kabasuka tombe twabo.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Yesu walengila mubwato bumo ubo bwalikuba bwa Shimoni, neye walasengeti abunyakileko pa lwenje. Walekala mubwato nekutatika kwiyisha bantu.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Mpwalapwisha kwiyisha, walambila Shimoni eti, “Bunyakileni bwato pakati, kwambeti muwale tombe twenu mumenshi mwikate inswi.”
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Shimoni walakumbuleti, “Shikwiyisha, kufuma mashiku bulatucele tuliya kwikatapo inswi, pakwinga mulamba njamwe ningwale tombe.”
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Lino balawala tombe twabo, nekwikata inswi shingi, tombe twabo twalatatika kupasuka.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Lino balakuwa banabo balikuba mubwato bumbi kwambeti bese babanyafweko kusabula, naboyo balesa, nomba balesusha mato abili nkayanda kwibila.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Shimoni Petulo mpwalaboneco walasuntama pantangu pa Yesu nekwambeti, “Kamundekelela Mwami Pakwinga ndeshikwinsa byaipa.”
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Shimoni ne banendi balenseco pakwinga balakankamana pa kufula kwa inswi isho nshobalekata.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Neco Jemusi ne Yohane bana bendi Zebediya kayi nebanendi Shimoni, naboyo balakankamana. Lino Yesu walambila Shimoni eti, “Kotatina pakwinga kufuma lelo nube weshikwikata bantu.”
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Popelapo balatanta mato ayo kuya kutala kwa mulonga, balashiya byonse nekunkokela Yesu.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Yesu mpwalikuba mumunshi naumbi walakumana ne muntu wali kukolwa bulwashi bwa mankuntu mubili wonse. Mpwalabona Yesu mulwashi uyu walasuntama kuntangu nekumusengeti, “Mwami ndicishi kwambeti mukute ngofu shakusengula nsenguleni.”
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Yesu walatandabula likasa lyakendi, walamwikata ne kwambeti, “Ee ndayandanga, koba cena!” Popelapo mankuntu alapwa.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Kufumapo Yesu walamwambileti, “Konyumfwa, kotambila muntu nambi umo makani awa. Nomba obe ululame wenga kuli beshikwiyisha, uyenga ulileshe kuli beshimilumbo kwambeti ulaba cena. Uye ubenge bupe kwelana ne ncalamba Mose kwambeti bantu bashometi ulaba cena.”
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Necikabeco impuwo ya Yesu yalanyumfwika kubantu bangi. Neco bantu balikwisa kuli endiye kwambeti banyumfwe Maswi akendi kayi nekubasengula malwashi abo.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Lino nendi Yesu walaya kwa enka akupaila.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Nabumbi busuba Yesu walikeyisha, popelapo palikuba Bafalisi ne beshikwiyisha milawo nabambi. Bantu aba balafuma muminshi yonse ya ku Galileya, ku Yudeya kayi neku Yelusalemu. Ngofu sha Lesa shalikuba muli Yesu kwambeti abasengule.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Kufumapo bantu nabambi balaleta mutuloba walikuba watontola mubili nkabali bamunyamuna pa mpasa. Balelesha kwambeti bamwingishe mu ng'andeti bamoneke pantangu pa Yesu.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Naboyo balikuyanda kumwingishila pacishinga, lino pakwinga bantu balafula balalilwa kwambeti bamutwale mukati. Neco balatanta nendi pa ciluli ca ng'anda ne kupasula mulyango, balamwingisha ne kumulelesha pampasa yakendi pakati pabantu ne kumushikisha pantangu pa Yesu.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Yesu mpwalabona kushoma kwakendi, “Walambeti, bwipishi bwakobe bulalekelelwa.”
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Lino beshikwiyisha Milawo kayi ne Bafalisi balatatika kwipushaneti, “Nomba uyu niyani lanyashanga Lesa? Niyani welela kulekelela bwipishi sena nte Lesa enka?”
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Lino Yesu walenshiba ncobalikuyeya mumyoyo yabo neku bepusheti, “Nomba mulayeyelenga cani bintu bya mushoboyo mu myoyo yenu?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Nicipeyo capuba kwambila muntu eti, ‘Bwipishi bwakobe bulalekelelwa,’ Nambi kwambeti, ‘Nyamuka, wende’
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Lino ndayandanga kumwambileti mwinshibe kwambeti mwana muntu ukute ngofu shakulekelela bwipishi pacishi ca panshi.” Kufumapo walambila usa watontola mubileti, “Ndakwambilinga, nyamuka, manta mpasa yakobe wenga kucomwenu.”
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Popelapo walapunduka bonse kabalanga nemenso abo, walamanta mpasa mpwalikuba wona nekutatika kuya nkalumbaisha Lesa.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Bantu bonse balakankamana kayi balatina. Lino balatatika kulumbaisha Lesa ne kwambeti, “Ici ncotulabono lelo, nkatutana tucibonapo sobwe.”
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Popelapo Yesu walafuma pansa nekubona weshikusonkesha musonko walikukwiweti Levi, nkali ekala mu ng'anda yamusonko. Yesu walamwambileti, “Nkonkele.”
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Popelapo neye walanyamuka, nekushiya byonse nekumukonkela.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Lino Levi walabamba byakulya bingi kwambeti basekelele ne Yesu mu ng'anda yakendi. Kwalikuba beshikusonkesha misonko bangi ne bantu nabambi kabalya pamo.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Bafalisi nabambi ne beshikwiyisha milawo balatatika kudandaulila beshikwiya ba Yesu eti, “Nomba nicani mulalyelenga nekunwa pamo ne beshikusonkesha kayi ne bantu babwipishi?”
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Lino Yesu walabakumbuleti, “Bayumi nkabakute kulangaula mu ng'anga sobwe, nsombi balwashi.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Ndiya kwishila balulama nsombi babwipishi kwambeti basanduke mu myoyo yabo.”
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Bantu nabambi balepusha Yesu eti, “Beshikwiya ba Yohane mubatishi bali kuba necindi cakulikanisha kulya nekupaila, naboyo beshikwiya ba Bafalisi bangi balikwinsa copeleco, bakobe baliya cindi camushoboyo, balo bakute kulya ne kunwowa.”
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Lino Yesu walabakumuleti, “Sena balikubwinga ingamubakakatisha kutalya nebanabo, shibwinga kacilipo? Sobwe!
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Nsombi cindi nicikashike shibwinga mpoti bakamufunyepo pali endibo, Lino ico cindi nibakalikanishe kulya.”
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Kufumapo Yesu walabambila cikoshanisho eti, “Kuliya muntu welela kukwamuna cimami cacikwisa caina nekutunga pa cakufwala cakeendi. Nkela kwinseco pakwinga naco ngacononga cikwisa kayi cimami nkacela kwendelana pacakufwala ico sobwe.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Kuliya muntu welela kubika waini walino lino munkomwa yacipaya cakendi. Nalabikimo waini walino lino ukute kupasula nkomwa. Waini wonse ngawitika ne konongeka.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Nomba waini walino lino welela kubikiwa mucinkuli calino lino.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Kuliya muntu welela kuyanda kunwa waini walino lino na lanu waini wakaindi pakwinga mukute kwambeti, ‘Usa wakaindi ewaina.’”
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luka 5 >