< Luka 5 >

1 Zgodí se pa, ko ga ljudstvo obsuje, da bi poslušali besedo Božjo, pa je on stal pri jezeru Genezaretskem.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 In ugleda dve ladji, da stojite ob jezeru; a ribiči so bili izšli iž njih in so izpirali mreže.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 In stopivši v eno od ladij, ktera je bila Simonova, zaprosi ga, naj malo odrine od kraja; ter sede, in učil je iz ladje ljudstvo.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 A ko neha govoriti, reče Simonu: Odrini na globoko, in vrzite mreže svoje na lov.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 In odgovarjajoč Simon, reče mu: Učenik, vso noč smo se trudili, in nič nismo vjeli; ali po besedi tvojej vrgel bom mrežo.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 In storivši to, zajemó veliko število rib; trgala pa jim se je mreža.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Ter pomignejo tovarišem, kteri so bili v drugej ladji, naj jim pridejo pomagat. Ter pridejo, in napolnijo obe ladji, da ste se topili.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Vidveši pa to Simon Peter, pade h kolenom Jezusovim, govoreč: Izidi od mene, ker sem človek grešnik, Gospod!
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Kajti groza je bila obšla njega in vse, kteri so bili ž njim, od vlaka rib, ki so ga bili zajeli.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Ravno tako pa tudi Jakoba in Janeza, sinova Zebedejeva, ktera sta bila tovariša Simonova. Pa reče Jezus Simonu: Ne boj se! odslej boš ljudí lovil.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 In potegnivši ladjo h kraju, popusté vse, in odidejo za njim.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 In zgodí se, ko je bil v enem mestu, in glej, mož ves v gobi; in ugledavši Jezusa, pade na obraz, in prosil ga je, govoreč: Gospod, če hočeš, moreš me očistiti.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 In stegnivši roko, dotakne se ga, in reče: Hočem, očisti se! In precej je odšla goba od njega.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 In on mu naroči, naj nikomur ne pové; nego pojdi, reče mu, pokaži se duhovnu, in prinesi za očiščenje svoje, kakor je ukazal Mojzes, njim za pričo.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Ali razglaševala se je le še s tem bolj govorica o njem; in stekalo se je veliko ljudstva, da bi ga poslušali, in da bi jih uzdravljal od njih bolezni.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 A on je odhajal v puščave in je molil.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 In zgodí se en dan, in on je učil; in sedeli so tam Farizeji in učeniki postave, kteri so bili prišli iz vseh vasi Galilejskih in Judejskih in Jeruzalema; in moč Gospodova je bila, da jih je uzdravljala.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 In glej, možjé prinesó na odru človeka, kteri je bil mrtvouden, in iskali so, kako bi ga vnesli in položili pred-nj.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 In ko ne najdejo, kod bi ga vnesli, za voljo ljudstva, zlezejo na streho, in skozi skodle spusté ga z odrom na sredo pred Jezusa.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 In videvši njih vero, reče mu: Človek, odpuščajo ti se grehi tvoji.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Pa začnó premišljati pismarji in Farizeji, govoreč: Kdo je ta, da preklinja Boga? Kdo more odpuščati grehe, razen edini Bog!
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Spoznavši pa Jezus njih misli, odgovorí in jim reče: Kaj premišljate v srcih svojih?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Kaj je laže, reči: Odpuščajo ti se grehi tvoji? ali reči: Vstani in hodi?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Da boste pa vedeli, da ima oblast sin človečji na zemlji odpuščati grehe, (reče mrtvoudnemu: ) Tebi pravim, vstani in vzemi oder svoj, in pojdi na dom svoj.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 In precej vstane pred njimi, in vzeme, na čemer je ležal, in odide na dom svoj, hvaleč Boga.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 In groza obide vse, in hvalili so Boga, in napolnijo se strahú, govoreč: Čudne rečí smo videli danes.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 In po tem izide, in ugleda mitarja, po imenu Levija, da sedí na mitnici, in reče mu: Pojdi za menoj!
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 In pustivši vse, vstane in odide za njim.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 In napravi mu Levij veliko pojedinjo v hiši svojej; in bila je velika množica mitarjev, in drugih, kteri so ž njimi sedeli za mizo.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 In godrnjali so pismarji in Farizeji, govoreč učencem njegovim: Za kaj z mitarji in grešniki jeste in pijete?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 In odgovarjajoč Jezus, reče jim: Ne potrebujejo zdravi zdravnika, nego bolni.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Nisem prišel klicat pravičnih, nego grešnike na pokoro.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 A oni mu rekó: Po kaj se učenci Janezovi pogostoma postijo, in molijo, tako tudi Farizejski; tvoji pa jedó in pijejo?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 On jim pa reče: Morete li storiti, da bi se svatje, dokler je ženin ž njimi, postili?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Prišli bodo pa dnevi, in ko jim se bo ženin odvzel, tedaj se bodo postili v tistih dnéh.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Pravil jim je pa tudi priliko: Nikdor zaplate od nove obleke ne prišiva na staro obleko; sicer bo tudi novo razdrl, in starej se ne prilega zaplata od nove.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 In nikdor ne deva novega vina v stare mehove; sicer predere vino nove mehove, in ono se izlije, in mehovi se pokazé;
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Nego novo vino se mora v nove mehove vlijati, in oboje se ohrani.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 In kdor je pil staro, nikdar ne če precej novega; ker pravi: Staro je bolje.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luka 5 >