< Luka 1 >

1 Ko so mnogi jeli opisovati rečí, ktere so popolnoma gotove med nami,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Kakor so nam izročili, kteri so od začetka sami videli in so služabniki besede bili:
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Namenil sem tudi jaz, ki sem vse od začetka na tanko pozvedel, po vrsti pisati tebi, častiti Teofil!
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Da spoznaš gotovost rečî, kterih si se naučil.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Bil je v dnéh Heroda kralja Judejskega neki duhoven po imenu Zaharija, od reda Abijevega; in žena njegova od hčeri Aronovih, in ime jej je bilo Elizabeta.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Bila sta pa oba pravična pred Bogom, in živela sta po vseh zapovedih in ustavah Gospodovih brez madeža.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 In nista imela otrók, ker je bila Elizabeta nerodovitna, in oba sta se bila uže postarala.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Zgodí se pa, ko je po vrsti reda svojega služil pred Bogom,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Po navadi duhovstva zadene ga opravilo, naj vnide v tempelj Gospodov, da pokadí.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 In vsa množiča ljudstva je bila zunej, in molila je v čas kajenja.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Prikaže pa mu se angelj Gospodov, stoječ na desnej strani kadilnega oltarja.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 In Zaharija se ustraši, ko ga ugleda, in groza ga obide.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Angelj mu pa reče: Ne boj se, Zaharija! kajti uslišana je molitev tvoja, in žena tvoja Elizabeta ti bo rodila sina, in imenuj ime njegovo Janez.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 In bo ti na radost in na veselje, in veliko se jih bo rojstvu njegovemu radovalo.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Kajti velik bo pred Gospodom; in vina in močne pijače ne bo pil, in napolnil se bo Duha svetega še v telesu matere svoje.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 In veliko sinov Izraelskih bo obrnil h Gospodu Bogu njih.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 In on pojde pred njim z duhom in močjó Elijevo, da obrne srca očetov k otrokom, in nevernike k razumnosti pravičnih: da pripravi Gospodu ljudstvo gotovo.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Pa reče Zaharija angelju: Po čem bom poznal to? kajti jaz sem star, in žena moja se je postarala.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 In odgovarjajoč angelj, reče mu: Jaz sem Gabrijel, ki stojim pred Bogom, in poslan sem, naj s teboj govorim, in ti to veselje oznanim.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 In glej, mutast boš in ne boš mogel govoriti do dné, ko se bo to zgodilo; ker nisi veroval besedam mojim, ktere se bodo izpolnile o svojem času.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 In čakalo je ljudstvo Zaharija; in čudili so se, da se tako dolgo mudí v tempeljnu.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Ko pa izide, ni jim mogel govoriti? in spoznajo, da je videl prikazen v tempeljnu: in on jim je pomigaval, in ostal je mutast.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 In zgodí se, ko se izpolnijo dnevi službe njegove, odide na dom svoj.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 A po teh dnéh je Elizabeta žena njegova spočela, in skrivala se je pet mesecev, govoreč:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Tako mi je storil Gospod v dnéh, ko se je ozrl na me, da odvzeme oponos moj med ljudmí.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 A šesti mesec pošlje Bog angelja Gabrijela v mesto Galilejsko, kteremu je ime Nazaret,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 K devici zaročenej možu, kteremu je bilo ime Jožef, iz hiše Davidove; in devici je bilo ime Marija.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 In angelj vnide k njej, in reče: Zdrava, z milostjo obdarovana! Gospod je s teboj; blagoslovljena si ti med ženami.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Ona pa, ko ga ugleda, prestraši se od besede njegove, in premišljevala je, kakošen bi bil ta pozdrav.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Pa jej angelj reče; Ne boj se, Marija! našla si namreč milost pri Bogu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 In glej, spočela boš v telesu, in rodila boš sina, in imenuj ime njegovo Jezus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Ta bo velik, in imenoval se bo sin najvišega; in dal mu bo Gospod Bog prestol Davida očeta njegovega,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 In kraljeval bo v hiši Jakobovej vekomaj, in kraljestvu njegovemu ne bo konca. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Marija pa reče angelju: Kako bo to, ko moža ne poznam?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 In odgovarjajoč angelj, reče jej; Sveti Duh bo prišel na te, in moč najvišega te bo obsenčila; za to se bo sveto, ktero se bo rodilo iz tebe, imenovalo sin Božji.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 In glej, Elizabeta teta tvoja, tudi ona je spočela sina v starosti svojej; in ta mesec jej je šesti, njej, ki jo imenujejo nerodovitno:
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Ker ne bo nobene besede pri Bogu, ktera se ne bi mogla izpolniti.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Marija pa reče: Glej, dekla sem Gospodova; zgôdi mi se po besedi tvojej. In angelj odide od nje.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Vstavši pa Marija v té dni, odide jadrno na gorenjo stran v mesto Judovo.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 In vnide v hišo Zaharijevo, in pozdravi Elizabeto.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 In zgodí se, ko sliši Elizabeta pozdrav Marijin, zaigra dete v telesu njenem; in Elizabeta se napolni Duha svetega,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 In zavpije z močnim glasom, in reče: Blagoslovljena si ti med ženami, in blagoslovljen je sad telesa tvojega.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 In odkod meni to, da je prišla mati Gospoda mojega k meni?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Kajti glej, ko je prišel glas pozdrava tvojega v ušesa moja, zaigralo je dete radostno v telesu mojem.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 In blagor jej, ktera je verovala; kajti zgodilo se bo, kar jej je rekel Gospod.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Pa reče Marija: Duša moja poveličuje Gospoda,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 In duh moj se je oveselil v Bogu, zveličarji mojem:
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Da se je ozrl na ponižanje dekle svoje. Kajti glej, odslej me bodo blagrovali vsi rodovi:
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Ker mi je storil velike rečí on, ki je mogočen, in ime njegovo sveto;
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 In usmiljenje njegovo od roda do roda tistim, kteri se ga bojé.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Pokazal je moč z roko svojo: razkropil je ošabne v mislih srca njih;
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Vrgel je mogočne s prestola, in povišal je ponižne.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Lačne je napolnil z blagom, in bogate je odpravil prazne.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Sprejel je Izraela hlapca svojega, da se spomene usmiljenja svojega.
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 (Kakor je govoril očetom našim, ) Abrahamu in semenu njegovemu na vekomaj. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Prebila je pa Marija ž njo kake tri mesece; in vrne se na dom svoj.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 A Elizabeti se izpolni čas, da porodí, in rodí sina.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 In sosedje in sorodniki njeni zaslišijo, da je pokazal Gospod veliko usmiljenje svoje na njej; in radovali so se ž njo.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 In zgodí se osmi dan, da pridejo deteta obrezovat; in klicali so ga po imenu očeta njegovega, Zaharija.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Ali odgovarjajoč mati njegova, reče: Ne, nego imenoval se bo Janez.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 In rekó jej: Nikogar ni v rodovini tvojej, da bi mu bilo tako ime.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 In pomigavali so očetu njegovemu, kako hoče, da bi ga imenovali.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 In izprosivši tablico, napiše, govoreč: Janez mu je ime. In vsi se začudijo.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 In odprla so se usta njegova pri tej priči in jezik njegov, in govoril je, hvaleč Boga.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 In strah obide vse njih sosede; in po vsej gorenjej Judeji se razglasé vse te reči.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 In vsi, kteri jih slišijo, položé jih v srce svoje, govoreč: Kaj neki bo iz tega otroka? In roka Gospodova je bila ž njim.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 In Zaharija oče njegov se napolni Duha svetega, in prerokuje, govoreč:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blagoslovljen Gospod Bog Izraelov, da je obiskal in odrešil ljudstvo svoje;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 In nam povzdignil rog zveličanja v hiši Davida hlapca svojega,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (Kakor je govoril z ustmi svetih prerokov svojih, ki so bili od nekedaj: ) (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Da nas bo rešil sovražnikov naših in iz rok vseh, kteri nas mrzé:
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Da storí usmiljenje očetom našim, in se spomene svete zaveze svoje,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Prisege, ktero je prisegel Abrahamu očetu našemu, da nam bo dal,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Da mu, rešeni iz rok sovražnikov svojih, brez straha služimo,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 V svetosti in pravičnosti pred njim vse svoje žive dní.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 In ti, otrok, imenoval se boš prerok najvišega; kajti šel boš pred obličjem Gospodovim, da mu pripraviš pot;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 In daš razum zveličanja ljudstvu njegovemu za odpuščanje njih grehov,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Po prisrčnem usmiljenji Boga našega, po kterem nas je obiskal vzhod z vižave:
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Da obsije tiste, kteri sedé v temi in smrtnej senci; da naravná noge naše na pot mirú.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 A dete je rastlo in se krepčalo v duhu; in bilo je v puščavah do dné, ko se pokaže Izraelu.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luka 1 >