< Luka 9 >

1 Potem je sklical skupaj svoje dvanajstere učence in jim dal moč in oblast nad vsemi hudiči in za ozdravljanje bolezni.
Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
2 In poslal jih je, da oznanjajo Božje kraljestvo in da ozdravljajo bolne.
Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3 Rekel jim je: »Za svoje potovanje ne vzemite ničesar, niti palic, prav tako ne malhe, niti kruha, niti denarja, niti ne imejte vsak po dva plašča.
Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
4 In v katerokoli hišo vstopite, tam ostanite in od tam odidite.
Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
5 Kdorkoli vas ne bo sprejel, kadar greste iz tega mesta, si iz svojih stopal otresite prav [ta] prah, v pričevanje proti njim.«
In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
6 In odpravili so se in šli skozi mesta in oznanjali evangelij in povsod ozdravljali.
Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
7 Torej Herod, vladar četrtinskega dela province, je slišal o vsem, kar je bilo storjeno po njem; in bil je zmeden, zato ker so nekateri rekli, da je bil Janez obujen od mrtvih,
Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
8 in od nekaterih, da se je pojavil Elija in od drugih, da je vstal eden izmed starih prerokov.
waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
9 Herod pa je rekel: »Janeza sem jaz obglavil, toda kdo je ta, o katerem slišim takšne stvari?« In želel si je, da bi ga videl.
Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
10 In apostoli, ko so se vrnili, so mu povedali vse, kar so storili. In vzel jih je in odšel stran, na samo, v zapuščen kraj, ki je pripadal mestu z imenom Betsajda.
Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
11 Ko je množica to izvedela, mu je sledila in sprejel jih je ter jim govoril o Božjem kraljestvu in ozdravil te, ki so imeli potrebo po ozdravljenju.
Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
12 In ko je dan začel minevati, potem so prišli dvanajsteri ter mu rekli: »Pošlji množico proč, da lahko gredo v mesta in naokoli po deželi ter prenočijo in si preskrbijo živeža, kajti tukaj smo na samotnem kraju.«
Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
13 Toda rekel jim je: »Vi jim dajte jesti.« Oni pa so rekli: »Nimamo več kot pet hlebov in dve ribi, razen, če bi šli in za vse te ljudi kupili hrano.«
Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
14 Kajti bilo jih je okoli pet tisoč mož. In svojim učencem je rekel: »Primorajte jih, da se usedejo v skupine po petdeset.«
Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
15 In storili so tako in vse so primorali sesti.
Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
16 Tedaj je vzel pet hlebov in dve ribi in jih, zroč k nebu, blagoslovil in razlomil in dal učencem, da jih postavijo pred množico.
Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
17 In jedli so in vsi so bili nasičeni. In od odlomkov, ki so jim ostali, je bilo nabranih dvanajst košar.
Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
18 In pripetilo se je, ko je bil sam in molil, [da] so bili z njim njegovi učenci. In vprašal jih je, rekoč: »Kdo pravi množica, da sem jaz?«
Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
19 Rekli so in odgovorili: »›Janez Krstnik, ‹ toda nekateri pravijo: ›Elija‹ in drugi pravijo, da je vstal eden izmed starih prerokov.«
Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
20 Rekel jim je: »Toda kdo vi pravite, da sem jaz?« Peter mu reče in odgovori: »Kristus od Boga.«
“Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
21 In strogo jim je naročil in jim ukazal, da te besede ne povedo nobenemu človeku,
Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
22 rekoč: »Sin človekov mora pretrpeti mnoge stvari in biti zavrnjen od starešin in visokih duhovnikov in pisarjev in umorjen bo in tretji dan bo obujen.«
Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
23 Njim vsem pa je rekel: »Če hoče katerikoli človek priti za menoj, naj se odpove samemu sebi in vsak dan vzame svoj križ ter mi sledi.
Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
24 Kajti kdorkoli hoče rešiti svoje življenje, ga bo izgubil, toda kdorkoli hoče izgubiti svoje življenje zaradi mene, ta isti ga bo rešil.
Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
25 Kajti kaj človeku koristi, če si pridobi ves svet, pa izgubi samega sebe ali je zavržen?
Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
26 Kajti kdorkoli se bo sramoval mene in mojih besed, njega se bo sramoval Sin človekov, ko bo prišel v svoji lastni slavi in v [slavi] svojega Očeta in svetih angelov.
Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
27 Toda povem vam po resnici, tam bo nekaj tukaj navzočih, ki ne bodo okusili smrti, dokler ne bodo videli Božjega kraljestva.«
“Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
28 In pripetilo se je okoli osmega dne po teh govorih, da je vzel Petra in Janeza in Jakoba ter odšel gor na goro, da moli.
Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
29 In medtem ko je molil, je bil videz njegovega obličja predrugačen in njegova oblačila so bila bela in sijoča.
Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
30 In glej, z njim sta govorila dva moža, ki sta bila Mojzes in Elija.
Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
31 Prikazala sta se v slavi in govorila o njegovem odhodu, ki naj bi ga dovršil v Jeruzalemu.
Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
32 Toda Peter in ta dva, ki sta bila z njim, so bili obteženi s spanjem. Ko so se zbudili, so videli njegovo slavo in dva moža, ki sta stala z njim.
Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
33 In pripetilo se je, ko sta odšla od njega, da je Peter rekel Jezusu: »Učitelj, dobro je za nas, da smo tukaj. Naredimo tri šotore: enega zate in enega za Mojzesa in enega za Elija, « pa ni vedel, kaj je govoril.
Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
34 Medtem ko je tako govoril, je prišel oblak in jih zasenčil in ko so vstopili v oblak, so se prestrašili.
Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
35 In iz oblaka je prišel glas, rekoč: »Ta je moj ljubljeni Sin, njega poslušajte.«
Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
36 In ko je glas minil, se je Jezus znašel sam. Oni pa so [to] obdržali zase in v tistih dneh nobenemu človeku niso povedali o teh stvareh, ki so jih videli.
Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
37 In pripetilo se je, da ga je naslednji dan, ko so prišli dol s hriba, srečalo mnogo ljudi.
Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
38 In glej, mož iz skupine je zavpil, rekoč: »Učitelj, rotim te, poglej na mojega sina, kajti on je moj edini otrok.
Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
39 In glej, duh ga napada in nenadoma vpije in trga ga, da se ponovno peni in ko ga močno udari, odide od njega.
Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
40 In rotil sem tvoje učence, da ga izženejo iz njega, pa niso mogli.«
Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
41 Jezus pa odgovori in reče: »O neverni in sprevrženi rod, kako dolgo bom še z vami in vas prenašal? Privedi svojega sina sèm.«
Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
42 In ko je šele prihajal, ga je hudič vrgel dol ter ga trgal. In Jezus je oštel nečistega duha in ozdravil otroka ter ga ponovno izročil njegovemu očetu.
Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
43 In vsi so bili osupli nad mogočno Božjo močjo. Toda medtem ko so se vsi čudili ob vseh stvareh, ki jih je Jezus storil, je svojim učencem rekel:
Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
44 »Naj te besede prodrejo v vaša ušesa, kajti Sin človekov bo izročen v človeške roke.«
“Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
45 Toda tega govora niso razumeli in ta je bil skrit pred njimi, da ga niso zaznali in bali so se ga vprašati o tem govoru.
Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
46 Potem je med njimi nastalo razmišljanje, kdo izmed njih naj bi bil največji.
Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
47 In Jezus, zaznavajoč misel njihovega srca, je vzel otroka ter ga postavil poleg sebe
Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
48 ter jim rekel: »Kdorkoli bo tega otroka sprejel v mojem imenu, sprejema mene in kdorkoli bo sprejel mene, sprejema tistega, ki me je poslal, kajti kdor je najmanjši med vami vsemi, ta isti bo velik.«
Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
49 In Janez je odgovoril ter rekel: »Učitelj, nekoga smo videli v tvojem imenu izganjati hudiče in smo mu prepovedali, ker ne hodi skupaj z nami.«
Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
50 Toda Jezus mu je rekel: »Ne prepovejte mu, kajti kdor ni proti nam, je za nas.«
Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
51 In pripetilo se je, ko je prišel čas, da naj bi bil sprejet gor, se je on neomajno odločil, da gre v Jeruzalem
Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
52 in pred svojim obrazom je poslal poslance in ti so šli ter vstopili v vas Samarijanov, da pripravijo zanj.
Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
53 Oni pa ga niso sprejeli, ker je bil njegov obraz, kakor da hoče iti v Jeruzalem.
Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
54 In ko sta njegova učenca, Jakob in Janez, to videla, sta rekla: »Gospod, hočeš, da ukaževa ognju, da pride dol z neba in jih pogoltne, kakor je storil Elija?«
Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
55 Toda on se je obrnil in ju oštel ter rekel: »Vidva ne vesta, iz kakšne vrste duha sta.
Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
56 Kajti Sin človekov ni prišel, da pokonča človeška življenja, temveč, da jih reši.« In odšli so v drugo vas.
Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
57 In pripetilo se je, ko so šli po poti, da mu je nek človek rekel: »Gospod, sledil ti bom, kamorkoli greš.«
Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
58 In Jezus mu je rekel: »Lisice imajo luknje in ptice neba imajo gnezda, toda Sin človekov nima kam nasloniti svoje glave.«
Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
59 In drugemu je rekel: »Sledi mi.« Vendar je ta rekel: »Gospod, dovoli mi najprej, da grem in pokopljem svojega očeta.«
Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
60 Jezus mu je rekel: »Naj mrtvi pokopljejo svoje mrtve, ti pa pojdi in oznanjaj Božje kraljestvo.«
Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
61 Prav tako je rekel drugi: »Gospod, sledil ti bom, toda naj grem najprej in se poslovim od teh, ki so doma v moji hiši.«
Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
62 In Jezus mu je rekel: »Nihče, ki svojo roko položi na plug in gleda nazaj, ni primeren za Božje kraljestvo.«
Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”

< Luka 9 >