< Luka 17 >

1 Potem je rekel učencem: »Ni mogoče, da prestopki ne bi prišli, toda gorje tistemu, po katerem bodo prišli!
Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
2 Bolje bi bilo zanj, da bi bil mlinski kamen obešen okoli njegovega vratu, on sam pa vržen v morje, kakor da bi pohujšal enega od teh malčkov.
Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
3 Pazite se: ›Če se tvoj brat prekrši zoper tebe, ga oštej; če pa se pokesa, mu odpusti.
Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
4 In če se sedemkrat dnevno prekrši zoper tebe in se sedemkrat dnevno ponovno obrne k tebi, rekoč: ›Kesam se, ‹ mu boš odpustil.‹«
In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
5 In apostoli so rekli Gospodu: »Povečaj našo vero.«
Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
6 Gospod pa je rekel: »Če bi imeli vero kakor zrno gorčičnega semena, bi lahko rekli temu drevesu črne murve: ›Bodi izruvana s korenino in bodi posajena v morje‹ in bi vam bila pokorna.
Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
7 Toda kdo izmed vas, ki ima služabnika, ki orje ali pase živino, mu bo v kratkem, ko pride iz polja, rekel: ›Pojdi in sedi k obedu?‹
“In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
8 In ali mu ne bo raje rekel: ›Pripravi mi nekaj, da bom lahko večerjal in se opaši ter mi strezi, dokler se ne najem in napijem, potem pa boš ti jedel in pil?‹
Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
9 Mar se bo zahvalil temu služabniku, ker je storil stvari, ki so mu bile ukazane? Menim, da ne.
Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
10 Tako tudi vi, ko boste naredili vse te stvari, ki so vam ukazane, recite: ›Nekoristni služabniki smo. Naredili smo to, kar je bila naša dolžnost, da storimo.‹«
Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
11 In pripetilo se je, ko je šel v Jeruzalem, da je šel čez sredo Samarije in Galileje.
Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
12 In ko je vstopil v neko vas, ga je tam srečalo deset mož, ki so bili gobavi, ki so stali daleč stran
Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
13 in povzdignili so svoje glasove ter rekli: »Jezus, Učitelj, usmili se nas.«
suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
14 In ko jih je zagledal, jim je rekel: »Pojdite, pokažite se duhovnikom.« In pripetilo se je, da ko so šli, so bili očiščeni.
Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
15 In ko je eden izmed njih videl, da je bil ozdravljen, se je obrnil nazaj in z močnim glasom slavil Boga
Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
16 in pri njegovih stopalih je padel dol na svoj obraz in mu dal zahvalo; in ta je bil Samarijan.
Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
17 In Jezus odgovori ter reče: »Mar ni bilo tu deset očiščenih? Toda kje je onih devet?
Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
18 Nikogar ni najti, ki bi se vrnil, da izroči slavo Bogu, razen tega tujca.«
Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
19 In rekel mu je: »Vstani, pojdi svojo pot, tvoja vera te je naredila zdravega.«
Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 In ko so ga farizeji povprašali, kdaj naj bi prišlo Božje kraljestvo, jim je odgovoril in rekel: »Božje kraljestvo ne prihaja z opazovanjem,
Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
21 tudi ne bodo rekli: ›Glejte, tukaj!‹ ali: ›Glejte tam!‹ kajti glejte, Božje kraljestvo je znotraj vas.«
Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
22 Učencem pa je rekel: »Prišli bodo dnevi, ko boste želeli videti enega izmed dni Sina človekovega, pa ga ne boste videli.
Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
23 In govorili vam bodo: ›Glejte tukaj‹ ali: ›Glejte tam.‹ Ne hodite za njimi niti jim ne sledite.
Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
24 Kajti kakor bliskanje, ki zasveti iz enega konca pod nebom, sveti do drugega konca pod nebom, tako bo tudi Sin človekov na svoj dan.
Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
25 Toda najprej mora pretrpeti mnoge stvari in biti zavržen od tega rodu.
Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
26 In kakor je bilo v Noetovih dneh, takó bo tudi v dneh Sina človekovega.
“Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
27 Jedli so, pili, poročali so žene, dane so bile v zakon, vse do dne, ko je Noe vstopil v barko in je prišla poplava ter jih vse uničila.
Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
28 Podobno bo, kot je bilo v Lotovih dneh; jedli so, pili, kupovali, prodajali, sadili, zidali;
“Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
29 toda istega dne, ko je Lot odšel iz Sódome, sta z neba deževala ogenj in žveplo ter jih vse uničila.
Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
30 Točno takó bo na dan, ko se razodene Sin človekov.
“Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
31 Na tisti dan naj tisti, ki bo na hišni strehi in njegove stvari v hiši, ne pride dol, da jih vzame proč; in kdor je na polju, naj se prav tako ne vrača nazaj.
A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
32 Spomnite se Lotove žene.
Ku tuna fa da matar Lot!
33 Kdorkoli si bo prizadeval rešiti svoje življenje, ga bo izgubil; kdorkoli pa bo izgubil svoje življenje, ga bo ohranil.
Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
34 Povem vam, v tej noči bosta dva človeka na eni postelji; eden bo vzet, drugi pa puščen.
Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
35 Dve ženski bosta skupaj mleli; ena bo vzeta, druga pa puščena.
Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
36 Dva moža bosta na polju; eden bo vzet, drugi pa puščen.«
37 In odgovorili so mu ter rekli: »Kje, Gospod?« In on jim je rekel: »Kjerkoli je telo, tam bodo orli zbrani skupaj.«
Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”

< Luka 17 >