< Luka 1 >

1 Ker so že mnogi vzeli v roko, da po vrsti uredijo izjavo o teh stvareh, ki se najbolj gotovo verjamejo med nami,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 celo kakor so nam jih izročili [tisti], ki so bili od začetka priče in služabniki besede,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 se je tudi meni zdelo dobro, od samega začetka imeti popolno razumevanje o vseh stvareh, da tebi, nadvse odlični Teófil, napišem po vrsti,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 da lahko spoznaš zanesljivost o teh besedah, o katerih si bil poučen.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 V dneh Heroda, judejskega kralja, je bil nek duhovnik, imenovan Zaharija, iz Abíjeve skupine, in njegova žena je bila izmed Aronovih hčera in njeno ime je bilo Elizabeta.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Oba sta bila pravična pred Bogom in sta brez krivde živela po vseh Gospodovih zapovedih in odredbah.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Ker je bila Elizabeta jalova nista imela nobenega otroka in oba sta bila zelo zvrhana v letih.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 In pripetilo se je, medtem ko je pred Bogom opravljal duhovniško službo, po vrstnem redu svoje skupine,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 glede na navado duhovniške službe, je bil na njem žreb, da zažge kadilo, ko je odšel v Gospodov tempelj.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Celotna množica ljudi pa je ob času zažiganja kadila zunaj molila.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 In prikazal se mu je Gospodov angel, stoječ na desni strani kadilnega oltarja.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Ko pa ga je Zaharija zagledal, se je vznemiril in strah ga je spreletel.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Toda angel mu je rekel: »Ne boj se, Zaharija, kajti tvoja molitev je uslišana in tvoja žena Elizabeta ti bo rodila sina in ti boš klical njegovo ime Janez.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Imel boš radost in veselje in mnogi se bodo veselili ob njegovem rojstvu.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Kajti velik bo v Gospodovih očeh in ne bo pil niti vina niti močne pijače in celó od maternice svoje matere bo izpolnjen s Svetim Duhom.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 In mnoge izmed Izraelovih otrok bo obrnil h Gospodu, njihovemu Bogu.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Pred njim bo šel z Elijevim duhom in močjo, da obrne srca očetov k otrokom in neposlušne k modrosti pravičnih; da pripravi ljudstvo, pripravljeno za Gospoda.«
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zaharija je angelu rekel: »Po čem bom to spoznal? Kajti starec sem in moja žena je zelo zvrhana v letih.«
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Angel mu odgovori in reče: »Jaz sem Gabriel, ki stojim v prisotnosti Boga in poslan sem, da ti govorim in da ti pokažem te vesele novice.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Glej, ker nisi verjel mojim besedam, ki se bodo uresničile ob njihovem pravem času, boš postal nem in ne boš mogel govoriti do dne, ko se bodo te besede izpolnile.«
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 In ljudje so čakali na Zaharija in se čudili, da se je tako dolgo mudil v templju.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Ko pa je prišel ven, jim ni mogel spregovoriti, in zaznali so, da je videl v templju videnje, kajti dajal jim je znamenja, ostal pa je brez besed.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Pripetilo se je, kakor hitro so bili dnevi njegovega služenja dovršeni, da se je odpravil k svoji lastni hiši.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Po teh dneh je njegova žena Elizabeta spočela in se pet mesecev skrivala, rekoč:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 »Tako je Gospod ravnal z menoj v dneh, v katerih je pogledal name, da odvzame mojo grajo izmed ljudi.«
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 V šestem mesecu pa je bil od Boga poslan angel Gabriel v galilejsko mesto, imenovano Nazaret,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 k devici, zaročeni z možem, katerega ime je bilo Jožef, iz Davidove hiše; in devici je bilo ime Marija.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Angel je vstopil k njej in rekel: »Pozdravljena, ti, ki si zelo spoštovana, Gospod je s teboj, blagoslovljena si med ženskami.«
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Ko pa ga je zagledala, je bila ob njegovem govoru zaskrbljena in v svojih mislih preudarjala, kakšne vrste pozdrav naj bi to bil.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Angel ji je rekel: »Ne boj se, Marija, kajti pri Bogu si našla naklonjenost.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Glej, v svoji maternici boš spočela in rodila sina in njegovo ime boš klicala JEZUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Velik bo in imenovan bo Sin Najvišjega; in Gospod Bog mu bo dal prestol njegovega očeta Davida
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 in nad Jakobovo hišo bo vladal večno in njegovemu kraljestvu ne bo konca.« (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Potem je Marija rekla angelu: »Kako se bo to zgodilo, glede na to, da ne poznam moškega?«
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Angel je odgovoril in ji rekel: »Sveti Duh bo prišel nadte in moč Najvišjega te bo obsenčila, zato bo tudi ta sveta oseba, ki bo rojena od tebe, imenovana Božji Sin.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Glej, tvoja sestrična Elizabeta je prav tako v svoji visoki starosti spočela sina, in to je šesti mesec z njo, ki je bila imenovana jalova.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Kajti z Bogom nič ne bo nemogoče.«
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Marija je rekla: »Glej, Gospodova pomočnica; naj se mi zgodi glede na tvojo besedo.« In angel je odšel od nje.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Marija je v tistih dneh vstala in z naglico odšla v hribovito deželo, v Judovo mesto
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 in vstopila v Zaharijevo hišo ter pozdravila Elizabeto.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 In pripetilo se je, ko je Elizabeta zaslišala Marijin pozdrav, da je dete poskočilo v njeni maternici in Elizabeta je bila izpolnjena s Svetim Duhom
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 in zaklicala z močnim glasom ter rekla: »Blagoslovljena si ti med ženskami in blagoslovljen je sad tvoje maternice.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Od kod je meni to, da bi prišla k meni mati mojega Gospoda?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Kajti glej, brž ko je glas tvojega pozdrava zazvenel v mojih ušesih, je dete v moji maternici od radosti poskočilo.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Blagoslovljena je tista, ki je verovala, kajti izpolnile se bodo te besede, ki so ji bile povedane od Gospoda.«
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Marija je rekla: »Moja duša poveličuje Gospoda
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 in moj duh se veseli v Bogu, mojem Odrešeniku.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Kajti ozrl se je na nizek stan svoje pomočnice, kajti glej, odslej me bodo vsi rodovi imenovali blagoslovljeno.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Kajti tisti, ki je mogočen, mi je storil velike stvari in sveto je njegovo ime.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 In njegovo usmiljenje je od roda do roda nad tistimi, ki se ga bojijo.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 S svojim laktom je pokazal moč, ponosne je razgnal v domišljiji njihovih src.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Mogočne je odstranil z njihovih prestolov in povišal te z nizkim položajem.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Lačne je napolnil z dobrinami, bogate pa je odpustil prazne.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Pomagal je svojemu služabniku Izraelu, v spomin na svoje usmiljenje,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 kakor je govoril našim očetom, Abrahamu in njegovemu semenu na veke.« (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Marija je z njo ostala približno tri mesece in se vrnila v svojo lastno hišo.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Torej prišel je Elizabetin polni čas, ko naj bi rodila; in rodila je sina.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Njeni sosedje in njeni sorodniki so slišali, kako je Gospod nad njo izkazal veliko usmiljenje in veselili so se z njo.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Pripetilo pa se je, da so na osmi dan prišli, da obrežejo otroka in poimenovali so ga Zaharija, po imenu njegovega očeta.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Njegova mati pa je odgovorila in rekla: »Ne tako, temveč se bo imenoval Janez.«
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Oni pa so ji rekli: »Nikogar v tvojem sorodstvu ni, ki je poimenovan s tem imenom.«
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 In naredili so znamenja njegovemu očetu, kako bi ga on imenoval.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 In prosil je za pisalno deščico ter napisal, rekoč: »Njegovo ime je Janez.« In vsi so se čudili.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 In njegova usta so se takoj odprla in njegov jezik se je sprostil in spregovoril je ter hvalil Boga.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 In strah je prišel na vse, ki so prebivali naokoli njih; in vse te besede so se razglasile naokoli po vsej judejski hriboviti deželi.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 In vsi, ki so jih slišali, so si jih položili v svoja srca, rekoč: »Kakšne vrste otrok bo to!« In Gospodova roka je bila z njim.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 In njegov oče Zaharija je bil izpolnjen s Svetim Duhom in prerokoval, rekoč:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 »Blagoslovljen bodi Gospod, Izraelov Bog; kajti obiskal je in odkupil svoje ljudi
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 in za nas je dvignil rog rešitve duš v hiši svojega služabnika Davida,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 kakor je govoril po ustih svojih svetih prerokov, ki so bili, odkar je svet nastal, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 da bi bili mi lahko rešeni pred našimi sovražniki in iz roke vseh, ki nas sovražijo,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 da opravi usmiljenje, obljubljeno našim očetom in se spomni svoje svete zaveze,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 prisege, s katero je prisegel našemu očetu Abrahamu,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 da nam bo zagotovil, da mu bomo osvobojeni iz roke svojih sovražnikov, lahko služili brez strahu,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 v svetosti in pravičnosti pred njim, vse dni našega življenja.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Ti pa, otrok, boš imenovan prerok Najvišjega, kajti šel boš pred Gospodov obraz, da pripraviš njegove poti,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 da daš njegovim ljudem spoznanje o rešitvi duš z odpuščanjem njihovih grehov,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 po nežnem usmiljenju našega Boga; po katerem nas je obiskalo svitanje od zgoraj,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 da da svetlobo tem, ki sedijo v temi in v smrtni senci, da vodi naša stopala na pot miru.«
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Otrok pa je rasel in se krepil v duhu in bil je v puščavah do dneva njegove pojavitve Izraelu.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luka 1 >