< Ezekiel 22 >

1 Poleg tega je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 »Torej, človeški sin, ali boš sodil, ali boš sodil krvoločno mesto? Da, pokazal mu boš vse njegove ogabnosti.
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 Potem reci: ›Tako govori Gospod Bog: ›Mesto v svoji sredi preliva kri, da lahko pride njegov čas in zoper sebe izdeluje malike, da se omadežuje.
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 Postalo si krivo v svoji krvi, ki si jo prelilo; in omadeževalo si se s svojimi maliki, ki si jih naredilo; in svojim dnevom si povzročilo, da so se približali in prišlo si celó k svojim letom. Zato sem te naredil za grajo poganom in zasmeh vsem deželam.
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Tisti, ki so blizu in tisti, ki so daleč od tebe, te bodo zasmehovali, ki so neslavni in precej nadležni.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Glej, Izraelovi princi, vsak je bil v tebi k njihovi moči, da preliva kri.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 V tebi so prezirali očeta in mater. V tvoji sredi so z zatiranjem postopali s tujcem. V tebi so nadlegovali osirotelega in vdovo.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Preziralo si moje svete stvari in oskrunilo moje šabate.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 V tebi so ljudje, ki prenašajo govorice, da prelijejo kri; in v tebi jedo po gorah. V tvoji sredi zagrešujejo nespodobnost.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 V tebi so odkrili nagoto svojih očetov. V tebi so ponižali tisto, ki je bila oddvojena zaradi oskrunitve.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 In nekdo je zagrešil ogabnost z ženo svojega soseda; in drugi je opolzko omadeževal svojo snaho; in drugi je v tebi ponižal svojo sestro, hčer svojega očeta.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 V tebi so jemali darila, da prelijejo kri. Jemalo si obresti in donos in z izsiljevanjem si lakomno pridobivalo od svojih sosedov in si me pozabilo, ‹ govori Gospod Bog.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 ›Glej, zato sem udaril svojo roko ob tvoj nepošten dobiček, ki si ga naredilo in pri tvoji krvi, ki je bila v tvoji sredi.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Ali tvoje srce lahko prenese, ali so tvoje roke lahko močne v dneh, ko bom obračunal s teboj? Jaz, Gospod sem to govoril in bom to storil.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 In razkropil te bom med pogane in te razpršil v dežele in iz tebe použil tvojo umazanost.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 In vzelo boš svojo dediščino v sebi, pred očmi poganov in vedelo boš, da jaz sem Gospod.‹«
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 In k meni je prišla Gospodova beseda, rekoč:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 »Človeški sin, Izraelova hiša mi je postala žlindra. Vsi so bron, kositer, železo in svinec v sredi talilne peči; so celó srebrova žlindra.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 Zato tako govori Gospod Bog: ›Ker ste vsi postali žlindra, glejte, zato vas bom zbral v sredi [prestolnice] Jeruzalem.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 Kakor oni zbirajo srebro in bron in železo in svinec in kositer v sredi talilne peči, da nanjo pihajo ogenj, da to raztalijo; tako vas bom jaz zbral v svoji jezi in svoji razjarjenosti in vas bom pustil tam in vas raztalil.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 Da, zbral vas bom in pihal nad vas v ognju svojega besa in vi boste raztaljeni v njeni sredi.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 Kakor je srebro raztaljeno v sredi talilne peči, tako boste raztaljeni v njeni sredi in spoznali boste, da sem jaz, Gospod, nad vas izlil svojo razjarjenost.‹«
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 In k meni je prišla Gospodova beseda, rekoč:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 »Človeški sin, reci ji: ›Ti si dežela, ki ni očiščena niti ni nanjo deževalo na dan ogorčenja.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 Tam je zarota njenih prerokov v njeni sredi, podobna rjovenju leva, željnega plena. Požrli so duše, vzeli so zaklad in dragocene stvari; v njeni sredi so naredili mnogo vdov.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Njeni duhovniki so prekršili mojo postavo in oskrunili moje svete stvari. Niso pokazali nobene razlike med svetim in oskrunjenim niti niso pokazali razlike med nečistim in čistim in svoje oči so skrili pred mojimi šabati in jaz sem med njimi oskrunjen.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Njeni princi v njeni sredi so podobni volkovom, željnim plena, da prelijejo kri in da uničijo duše, da pridobijo nepošten dobiček.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 In njeni preroki so jih ometali z neutrjeno malto, gledoč ničnost in vedeževali so jim laži, rekoč: ›Tako govori Gospod Bog, ‹ ko Gospod ni govoril.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 Ljudstvo dežele je uporabljalo zatiranje in izvajalo rop in jezilo revne in pomoči potrebne; da, krivično so zatirali tujca.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 In iskal sem človeka med njimi, ki bi naredil ograjo in stal v razpoki pred menoj za deželo, da je ne bi uničil, toda nikogar nisem našel.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 Zato sem nadnje izlil svoje ogorčenje; použil sem jih z ognjem svojega besa. Njihovo lastno pot sem poplačal na njihovih glavah, ‹ govori Gospod Bog.‹«
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 22 >