< Откровение ап. Иоанна Богослова 10 >

1 И видех инаго Ангела крепка сходяща с небесе, оболчена во облак, и дуга над главою (его), и лице его яко солнце, и нозе его яко столпи огнени,
Sa'anan na ga wani babban mala'ika yana zuwa daga sama. Yana lullube cikin girgije, a bisa kansa akwai bakangizo. Fuskarsa kamar rana, kafafunsa kamar ginshikan wuta.
2 и имеяше в руце своей книгу разгибену: и постави ногу свою десную на мори, а шуюю на земли,
Yana rike da karamin littafi a hannunsa, da aka bude, sai ya sa kafarsa ta dama a bisa teku, kafarsa ta hagu kuma a kan kasa.
3 и возопи гласом великим, яко лев рыкая: и егда возгласи, глаголаша седмь громов гласы своя.
Sai yayi ihu da babbar murya kamar zaki mai ruri. Lokacin da ya yi ihu, tsawan nan bakwai suka yi magana da karar su.
4 И егда возгласиша седмь громов гласы своя, хотех писати: и слышах глас с небесе глаголющь ми: запечатлей, яже глаголаша седмь громов, и сего не пиши.
Da tsawan nan bakwai suka yi magana, ina dab da rubutu, amma na ji wata murya daga sama cewa, “Ka rike asirin abin da tsawan nan bakwai suka fada. Kada ka rubuta shi.”
5 И Ангел, егоже видех стояща на мори и на земли, воздвиже руку свою на небо
Sai mala'ikan da na gani tsaye bisa teku da kasa, ya daga hannun damarsa sama.
6 и клятся Живущим во веки веков, Иже созда небо и яже на нем, и землю и яже на ней, и море и яже в нем, яко лета уже не будет: (aiōn g165)
Sai ya rantse da wannan da ke raye har abada abadin - wanda ya halicci sama da duk abinda ke cikinsa, da duniya da duk abin da ke a kanta, da teku da dukan abin da ke cikinsa, sai mala'ikan ya ce, “Babu sauran jinkiri. (aiōn g165)
7 но во дни гласа седмаго Ангела, егда имать вострубити, тогда скончается тайна Божия, якоже благовести Своими рабы пророки.
Amma a ranar da mala'ika na bakwai yana dab da busa kahonsa, a lokacin ne asirin Allah zai cika, daidai da yadda ya sanar wa bayinsa annabawa.”
8 И глас его слышах с небесе паки глаголющь со мною, и глагола: иди и приими книжицу разгнутую в руце Ангела стоящаго на мори и на земли.
Muryar da na ji daga sama ta sake magana da ni: “Tafi, ka dauki budadden littafin da ke hannun mala'ikan da ke tsaye bisa teku da kan kasa.”
9 И идох ко Ангелу, глаголя ему: даждь ми книжицу. И рече ми: приими и снеждь ю: и горька будет во чреве твоем, но во устех ти сладка будет яко мед.
Sai na tafi wurin mala'ikan na ce da shi ka bani karamin littafin. Yace dani, “Dauki littafin ka ci. Zai sa cikinka ya yi daci, amma a bakinka zai yi zaki kamar zuma.”
10 И приях книгу от руки Ангела и снедох ю: и бе во устех моих яко мед сладка: и егда снедох ю, горька бяше во чреве моем.
Na dauki karamin littafin daga hannun mala'ikan na ci. Ya yi zaki sosai a bakina kamar zuma, amma da na ci, sai cikina ya zama da daci.
11 И рече ми: подобает ти паки пророчествовати в людех и во племенех, и во языцех и в царех мнозех.
Wani yace mani, “Dole ka sake yin annabci kuma game da mutane masu yawa, da al'ummai, da harsuna da sarakuna.”

< Откровение ап. Иоанна Богослова 10 >