< От Луки святое благовествование 1 >

1 Понеже убо мнози начаша чинити повесть о извествованных в нас вещех,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 якоже предаша нам, иже исперва самовидцы и слуги бывшии Словесе:
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 изволися и мне последовавшу выше вся испытно, поряду писати тебе, державный Феофиле,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 да разумееши, о нихже научился еси словесех утверждение.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Бысть во дни Ирода царя Иудейска, иерей некий, именем Захариа, от дневныя чреды Авиани: и жена его от дщерей Аароновех, и имя ей Елисаветь.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Беста же праведна оба пред Богом, ходяща во всех заповедех и оправданиих Господних безпорочна.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 И не бе има чада, понеже Елисаветь бе неплоды, и оба заматоревша во днех своих беста.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Бысть же служащу ему в чину чреды своея пред Богом,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 по обычаю священничества ключися ему покадити вшедшу в церковь Господню:
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 и все множество людий бе молитву дея вне, в год фимиама:
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 явися же ему Ангел Господень, стоя о десную олтаря кадилнаго:
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 и смутися Захариа видев, и страх нападе нань.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Рече же к нему Ангел: не бойся, Захарие: зане услышана бысть молитва твоя, и жена твоя Елисаветь родит сына тебе, и наречеши имя ему Иоанн:
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 и будет тебе радость и веселие, и мнози о рождестве его возрадуются:
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 будет бо велий пред Господем: и вина и сикера не имать пити, и Духа Святаго исполнится еще из чрева матере своея:
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 и многих от сынов Израилевых обратит ко Господу Богу их:
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 и той предидет пред Ним духом и силою Илииною, обратити сердца отцем на чада, и противныя в мудрости праведных, уготовати Господеви люди совершены.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 И рече Захариа ко Ангелу: по чесому разумею сие? Аз бо есмь стар, и жена моя заматоревши во днех своих.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 И отвещав Ангел рече ему: аз есмь Гавриил предстояй пред Богом, и послан есмь глаголати к тебе и благовестити тебе сия:
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 и се, будеши молчя и не могий проглаголати, до негоже дне будут сия: зане не веровал еси словесем моим, яже сбудутся во время свое.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 И беша людие ждуще Захарию: и чудяхуся коснящу ему в церкви.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Изшед же не можаше глаголати к ним: и разумеша, яко видение виде в церкви: и той бе помавая им, и пребываше нем.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 И бысть яко исполнишася дние службы его, иде в дом свой.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 По сих же днех зачат Елисаветь жена его, и таяшеся месяц пять, глаголющи:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 яко тако мне сотвори Господь во дни, в няже призре отяти поношение мое в человецех.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 В месяц же шестый послан бысть Ангел Гавриил от Бога во град Галилейский, емуже имя Назарет,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 к Деве обрученней мужеви, емуже имя Иосиф, от дому Давидова: и имя Деве Мариамь.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 И вшед к Ней Ангел рече: радуйся, Благодатная: Господь с Тобою: благословена Ты в женах.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Она же видевши смутися о словеси его и помышляше, каково будет целование сие.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 И рече Ангел Ей: не бойся, Мариамь: обрела бо еси благодать у Бога.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 И се зачнеши во чреве, и родиши Сына, и наречеши имя Ему Иисус:
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Сей будет велий, и Сын Вышняго наречется: и даст Ему Господь Бог престол Давида отца Его:
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 и воцарится в дому Иаковли во веки, и Царствию Его не будет конца. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Рече же Мариамь ко Ангелу: како будет сие, идеже мужа не знаю?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 И отвещав Ангел рече Ей: Дух Святый найдет на Тя, и сила Вышняго осенит Тя: темже и раждаемое Свято наречется Сын Божий:
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 и се, Елисаветь южика Твоя, и та зачат сына в старости своей: и сей месяц шестый есть ей нарицаемей неплоды:
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 яко не изнеможет у Бога всяк глаголгол.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Рече же Мариамь: се, Раба Господня: буди Мне по глаголу твоему. И отиде от Нея Ангел.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Воставши же Мариамь во дни тыя, иде в горняя со тщанием, во град Иудов:
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 и вниде в дом Захариин и целова Елисаветь.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 И бысть яко услыша Елисаветь целование Мариино, взыграся младенец во чреве ея: и исполнися Духа Свята Елисаветь,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 и возопи гласом велиим, и рече: благословена Ты в женах, и благословен плод чрева Твоего:
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 и откуду мне сие, да приидет Мати Господа моего ко мне?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Се бо, яко бысть глас целования Твоего во ушию моею, взыграся младенец радощами во чреве моем:
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 и блаженна Веровавшая, яко будет совершение глаголголанным Ей от Господа.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 И рече Мариамь: величит душа Моя Господа,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 и возрадовася дух Мой о Бозе Спасе Моем:
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 яко призре на смирение Рабы Своея: се бо, отныне ублажат Мя вси роди:
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 яко сотвори Мне величие Сильный, и свято имя Его:
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 и милость Его в роды родов боящымся Его:
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 сотвори державу мышцею Своею: расточи гордыя мыслию сердца их?
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Низложи сильныя со престол, и вознесе смиренныя:
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 алчущыя исполни благ и богатящыяся отпусти тщы:
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 восприят Израиля отрока Своего, помянути милости,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 якоже глагола ко отцем нашым, Аврааму и семени его до века. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Пребысть же Мариамь с нею яко три месяцы и возвратися в дом свой.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Елисавети же исполнися время родити ей, и роди сына.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 И слышаша окрест живущии и ужики ея, яко возвеличил есть Господь милость Свою с нею: и радовахуся с нею.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 И бысть во осмый день, приидоша обрезати отроча, и нарицаху е именем отца его, Захарию.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 И отвещавши мати его рече: ни, но да наречется Иоанн.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 И реша к ней, яко никтоже есть в родстве твоем, иже нарицается именем тем.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 И помаваху отцу его, еже како бы хотел нарещи е.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 И испрошь дщицу, написа, глаголя: Иоанн будет имя ему. И чудяхуся вси.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Отверзошася же уста его абие и язык его, и глаголаше благословя Бога.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 И бысть на всех страх живущих окрест их: и во всей стране Иудейстей поведаеми бяху вси глаголи сии.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 И положиша вси слышавшии в сердцы своем, глаголюще: что убо отроча сие будет? И рука Господня бе с ним.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 И Захариа отец его исполнися Духа Свята, и пророчествова, глаголя:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 благословен Господь Бог Израилев, яко посети и сотвори избавление людем Своим:
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 и воздвиже рог спасения нам, в дому Давида отрока Своего:
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 якоже глагола усты святых сущих от века пророк Его, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 спасение от враг наших и из руки всех ненавидящих нас:
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 сотворити милость со отцы нашими и помянути завет святый Свой,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 клятву, еюже клятся ко Аврааму отцу нашему, дати нам,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 без страха, из руки враг наших избавльшымся,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 служити Ему преподобием и правдою пред Ним вся дни живота нашего.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 И ты, отроча, пророк Вышняго наречешися: предидеши бо пред лицем Господним, уготовати пути Его,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 дати разум спасения людем Его, во оставление грех их,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 милосердия ради милости Бога нашего, в нихже посетил есть нас Восток свыше,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 просветити во тме и сени смертней седящыя, направити ноги нашя на путь мирен.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Отроча же растяше и крепляшеся духом: и бе в пустынех до дне явления своего ко Израилю.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< От Луки святое благовествование 1 >