< Книга Иисуса Навина 17 >

1 И быша пределы племене сынов Манассииных, яко сей первенец Иосифу, Махирови первенцу Манассиину, отцу Галаадову, (сей бо бысть муж храбр) в Галаадитиде и Васанитиде.
Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
2 И быша сыном Манассииным прочым по сонмом их: сыном Ахиезеровым и сыном Елековым и сыном Есриилевым, и сыном Сехемовым и сыном Семираеловым и сыном Оферовым: сии суть сынове Манассиины, сына Иосифова, мужеск пол по племеном своим.
Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
3 И Салпааду сыну Оферову, сына Галаадова, сына Махирова, сына Манассиина, не быша сыны, но токмо дщери: и сия имена дщерем Салпаадовым: Маала и Нуа, и Егла и Мелха и Ферса.
Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
4 И сташа пред Елеазаром жерцем и пред Иисусом сыном Навиным и пред князи, глаголющя: Бог заповеда рукою Моисеовою дати нам наследие посреде братии нашея. И дадеся им наследие повелением Господним, жребий в братии отца их.
Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
5 И паде жребий Манассию поле лавеково кроме земли Галаадовы и Васани, яже есть об ону страну Иордана,
Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
6 понеже дщери сынов Манассииных наследиша жребий посреде братий своих: земля же Галаадова бысть сыном Манассииным прочым.
domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
7 И быша пределы сынов Манассииных от Асир-Махфофа, и данаф, яже есть пред лицем Сихема, и идут пределы на Иамин и на Иасиф ко источнику Фаффоф.
Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
8 Манассию будет земля Фаффоф: и Фаффоф над пределы Манассииными сыном Ефремлим:
(Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
9 и снидут пределы к дебри Кана на юг по дебри Иарим: Теревинф Ефрему посреде града Манассиина. И пределы Манассиины к северу на водотечь, и будет исход его море:
Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
10 от юга Ефрему, и к северу Манассии, и будет море предел им: и ко Асиру совокупятся к северу, и Иссахару от восток.
Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
11 И будет Манассию (предел) между Иссахаром и между Асиром Вефсан и веси их, и Иевлаам и веси его, и живущыя в Доре и веси его, и живущыя в ендоре и веси его, и живущыя в Магедде и веси его, и живущыя в Танахе и веси его, и третия часть Нафефа и веси его.
A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
12 И не возмогоша сынове Манассиины потребити градов сих: и нача Хананей жити в земли сей.
Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
13 И бысть егда укрепишася сынове Израилевы, и сотвориша Хананеов послушных, потреблением же не потребиша их.
Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
14 Противореша же сынове Иосифовы Иисусу, глаголюще: почто наследствовал еси нас жребием единым и ужем единым? Аз же люд мног есмь, и благослови мя Бог (даже доселе).
Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
15 И рече им Иисус: аще люд мног еси, взыди в дубраву и отреби себе тамо место в земли Ферезеа и Рафаима, аще утесняет тя гора Ефремля.
Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
16 И реша сынове Иосифовы: не доволно нам горы Ефремли: и конь преизбранный и железо всему Хананею живущему в земли емек, в Вефсане и в весех ея, и во юдоле Иезраель.
Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
17 И рече Иисус к сыном Иосифовым, Ефрему и Манассию, глаголя: аще люд мног еси и силу велику имаши, не будет ти жребий един:
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
18 зане дубрава будет тебе, понеже дубрава есть, и отребиши ю, и будет тебе, и концы ея, егда потребиши Хананеа, аще конь преизбранный ему есть: (и сам силен, ) ты бо пресилиши его.
amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”

< Книга Иисуса Навина 17 >