< От Иоанна святое благовествование 4 >

1 Егда убо разуме Иисус, яко услышаша фарисее, яко Иисус множайшыя ученики творит и крещает, неже Иоанн:
Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
2 Иисус же Сам не крещаше, но ученицы Его:
ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
3 остави Иудею и иде паки в Галилею.
Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
4 Подобаше же Ему проити сквозе Самарию.
To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
5 Прииде убо во град Самарийский, глаголемый Сихарь, близ веси, юже даде Иаков Иосифу сыну своему:
Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
6 бе же ту источник Иаковль. Иисус же утруждся от пути, седяше тако на источнице: бе (же) яко час шестый.
Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
7 Прииде жена от Самарии почерпати воду. Глагола ей Иисус: даждь Ми пити.
Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
8 Ученицы бо Его отшли бяху во град, да брашно купят.
(Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
9 Глагола Ему жена Самаряныня: како ты Жидовин сый от мене пити просиши, жены Самаряныни сущей? Не прикасаютбося Жидове Самаряном.
Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
10 Отвеща Иисус и рече ей: аще бы ведала еси дар Божий, и Кто есть глаголяй ти: даждь Ми пити: ты бы просила у Него, и дал бы ти воду живу.
Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
11 Глагола Ему жена: господи, ни почерпала имаши, и студенец есть глубок: откуду убо имаши воду живу?
Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
12 Еда ты болий еси отца нашего Иакова, иже даде нам студенец сей, и той из него пит и сынове его и скоти его?
Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
13 Отвеща Иисус и рече ей: всяк пияй от воды сея, вжаждется паки:
Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
14 а иже пиет от воды, юже Аз дам ему, не вжаждется во веки: но вода, юже (Аз) дам ему, будет в нем источник воды текущия в живот вечный. (aiōn g165, aiōnios g166)
amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
15 Глагола к Нему жена: господи, даждь ми сию воду, да ни жажду, ни прихожду семо почерпати.
Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
16 Глагола ей Иисус: иди, пригласи мужа твоего и прииди семо.
Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
17 Отвеща жена и рече (Ему): не имам мужа. Глагола ей Иисус: добре рекла еси, яко мужа не имам:
Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
18 пять бо мужей имела еси, и ныне, егоже имаши, несть ти муж: се воистинну рекла еси.
Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
19 Глагола Ему жена: Господи, вижу, яко пророк еси Ты:
Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
20 отцы наши в горе сей поклонишася: и вы глаголете, яко во Иерусалимех есть место, идеже кланятися подобает.
Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
21 Глагола ей Иисус: жено, веру Ми ими, яко грядет час, егда ни в горе сей, ни во Иерусалимех поклонитеся Отцу:
Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
22 вы кланяетеся, егоже не весте: мы кланяемся, егоже вемы, яко спасение от Иудей есть:
Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
23 но грядет час, и ныне есть, егда истиннии поклонницы поклонятся Отцу духом и истиною: ибо Отец таковых ищет покланяющихся Ему:
Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
24 дух (есть) Бог: и иже кланяется Ему, духом и истиною достоит кланятися.
Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
25 Глагола Ему жена: вем, яко Мессиа приидет, глаголемыи Христос: егда Той приидет, возвестит нам вся.
Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
26 Глагола ей Иисус: Аз есмь, глаголяй с тобою.
Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
27 И тогда приидоша ученицы Его и чудяхуся, яко с женою глаголаше: обаче никтоже рече: чесо ищеши? Или: что глаголеши с нею?
Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
28 Остави же водонос свой жена, и иде во град, и глагола человеком:
Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
29 приидите (и) видите Человека, Иже рече ми вся, елика сотворих: еда Той есть Христос?
“Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
30 Изыдоша же из града и грядяху к Нему.
Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
31 Между же сим моляху Его ученицы (Его), глаголюще: Равви, яждь.
Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
32 Он же рече им: Аз брашно имам ясти, егоже вы не весте.
Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
33 Глаголаху убо ученицы к себе: еда кто принесе Ему ясти?
Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
34 Глагола им Иисус: Мое брашно есть, да сотворю волю Пославшаго Мя и совершу дело Его.
Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
35 Не вы ли глаголете, яко еще четыри месяцы суть, и жатва приидет? Се, глаголю вам: возведите очи ваши и видите нивы, яко плавы суть к жатве уже:
Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
36 и жняй мзду приемлет и собирает плод в живот вечный, да и сеяй вкупе радуется и жняй: (aiōnios g166)
Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios g166)
37 о сем бо слово есть истинное, яко ин есть сеяй, и ин (есть) жняй:
Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
38 аз послах вы жати, идеже вы не трудистеся: инии трудишася, и вы в труд их внидосте.
Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
39 От града же того мнози вероваша в Онь от Самарян, за слово жены свидетелствующия, яко рече ми вся, елика сотворих.
Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
40 Егда убо приидоша к Нему Самаряне, моляху Его, дабы пребыл у них: и пребысть ту два дни.
To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
41 И много паче вероваша за слово Его:
Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
42 жене же глаголаху, яко не ктому за твою беседу веруем: сами бо слышахом и вемы, яко Сей есть воистинну Спас миру, Христос.
Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
43 По двою же дню изыде оттуду и иде в Галилею:
Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
44 Сам бо Иисус свидетелствова, яко пророк во своем отечествии чести не имать.
(To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
45 Егда же прииде в Галилею, прияша Его Галилеане, вся видевше, яже сотвори во Иерусалимех в праздник: и тии бо приидоша в праздник.
Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
46 Прииде же паки Иисус в Кану Галилейскую, идеже претвори воду в вино. И бе некий царев муж, егоже сын боляше в Капернауме.
Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
47 Сей слышав, яко Иисус прииде от Иудеи в Галилею, иде к Нему и моляше Его, да снидет и исцелит сына Его: имеяше бо умрети.
Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
48 Рече убо Иисус к нему: аще знамении и чудес не видите, не имате веровати.
Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
49 Глагола к Нему царев муж: Господи, сниди, прежде даже не умрет отроча мое.
Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
50 Глагола ему Иисус: иди, сын твой жив есть. И верова человек словеси, еже рече ему Иисус, и идяше.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
51 Абие же входящу ему, (се, ) раби его сретоша его и возвестиша (ему), глаголюще, яко сын твой жив есть.
Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
52 Вопрошаше убо от них о часе, в который легчае ему бысть, и реша ему, яко вчера в час седмый остави его огнь.
Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
53 Разуме же отец, яко той бе час, в оньже рече ему Иисус, яко сын твой жив есть: и верова сам и весь дом его.
Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
54 Сие паки второе знамение сотвори Иисус, пришед от Иудеи в Галилею.
Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.

< От Иоанна святое благовествование 4 >