< Књига Немијина 2 >

1 А месеца Нисана године двадесете Артаксеркса цара беше вино пред њим, и ја узевши вино дадох га цару. А пре не бејах невесео пред њим.
A watan Nisan a shekara ta ashirin ta mulkin Sarki Artazerzes, sa’ad aka kawo masa ruwan inabi, sai na karɓa na ba shi. Ban taɓa ɓata fuskata a gabansa ba, sai wannan karo.
2 И рече ми цар: Што си лица невеселог, кад ниси болестан? Није друго него туга у срцу. А ја се уплаших врло.
Saboda haka sarki ya tambaye ni ya ce, “Me ya sa fuskarka ta ɓaci, ga shi, ba ciwo kake ba? Ba abin da ya kawo wannan, in ba dai kana baƙin ciki ba.” Sai na ji tsoro ƙwarai,
3 И рекох цару: Да је жив цар до века! Како не бих био лица невеселог, кад је град где су гробови мојих отаца опустео и врата му огњем спаљена?
na amsa na ce wa sarki, “Ran sarki yă daɗe! Me zai hana fuskata ta ɓaci, sa’ad da birnin da aka binne kakannina tana zaman kango, aka kuma rushe ƙofofinsa da wuta?”
4 А цар ми рече: Шта хоћеш? Тада се помолих Богу небеском,
Sai sarki ya ce mini, “Me kake so?” Sai na yi addu’a ga Allah na sama,
5 И рекох цару: Ако је угодно цару и ако ти је мио слуга твој, пошљи ме у Јудеју у град где су гробови отаца мојих да га саградим.
na kuwa ba wa sarki amsa, na ce, “In ya gamshi sarki, in kuma bawanka ya sami tagomashi a idonka, bari ka aike ni in tafi ƙasar Yahuda, birnin da aka binne kakannina, domin in sāke gina shi.”
6 А цар ми рече, а жена његова сеђаше до њега: Колико ти времена треба на пут, и кад ћеш се вратити? И би угодно цару, и пусти ме кад му казах време.
Sai sarki, a lokacin sarauniya da tana zama kusa da shi, ya tambaye ni, ya ce, “Kwana nawa tafiyar za tă ɗauke ka, kuma yaushe za ka dawo?” Ya gamshi sarki ya aike ni; saboda haka na shirya lokaci.
7 Потом рекох цару: Ако је угодно цару, да ми се да књига на кнезове преко реке да ме прате докле не дођем у Јудеју,
Na kuma ce masa, “In ya gamshi sarki, zai yi kyau in sami wasiƙu zuwa ga gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, domin su tanada kāriya har sai na isa Yahuda?
8 И књига на Асафа, чувара шуме цареве да ми да дрва за брвна на врата од двора уз дом Божји и за зид градски и за кућу у коју ћу ући. И даде ми цар, јер добра рука Бога мог беше нада мном.
A kuma ba ni wasiƙa zuwa ga Asaf, sarkin daji, yă ba ni katako don yin ƙofofin kagara na kusa da fadar haikali da kuma don katangar birni, da na wurin da zan zauna?” Sarki kuwa ya ba ni abin da na roƙa, gama Allah yana tare da ni.
9 И тако дођох са кнезовима преко реке, и дадох им књиге цареве. А цар посла са мном војводе и коњике.
Saboda haka na tafi wurin gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, na ba su wasiƙun sarki. Sarki kuma ya aika da hafsoshin mayaƙa da kuma mahayan dawakai tare da ni.
10 А кад то чу Санавалат Ороњанин и Товија, слуга Амонац, би им врло мрско што дође човек да се постара за добро синовима Израиљевим.
Da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon suka ji cewa wani ya zo domin yă ƙarfafa zaman lafiyar mutanen Isra’ila, sai suka damu ƙwarai.
11 Потом дођох у Јерусалим, и бих онде три дана.
Sai na je Urushalima, bayan na zauna a can na kwanaki uku,
12 Па устах ноћу с неколико људи, а ником не казах шта ми је Бог мој дао у срце да учиним у Јерусалиму; и не имах кљусета са собом осим оног на коме јахах.
sai na fita da dare tare da mutane kalila. Ban faɗa wa wani abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi don Urushalima ba. Ba waɗansu dabbobi kuma tare da ni, sai dai dabbar da na hau.
13 И изиђох ноћу на врата од долине, на извор змајевски, и на врата гнојна, и разгледах зидове јерусалимске како беху разваљени и како му врата беху огњем попаљена.
Da dare na fita ta Ƙofar Kwari wajen Rijiyar Dila da Ƙofar Juji, ina dudduba katangar Urushalima waɗanda aka rushe da kuma ƙofofinta waɗanda aka ƙone da wuta.
14 Отуда прођох на изворска врата и на царско језеро, а онде не беше места да кљусе пода мном пређе.
Sa’an nan na ci gaba zuwa wajen Ƙofar Maɓuɓɓuga da kuma Tafkin Sarki, amma babu isashen wuri saboda abin da na hau yă bi;
15 Зато јахах уз поток по ноћи и разгледах зид, па се вратих на врата од долине, и тако дођох натраг.
saboda haka na haura ta kwarin da dad dare, ina dudduba katangar. A ƙarshe, na juya na sāke shiga ta Ƙofar Kwari.
16 Али поглавари не знаху куда сам ишао ни шта сам радио, јер дотада не бејах ништа рекао ни Јудејцима ни свештеницима ни кнезовима ни поглаварима ни другима који управљаху послом.
Shugabanni ba su san inda na tafi, ko abin da nake yi ba, domin ban riga na faɗa wa Yahudawa, ko firistoci, ko manyan gari, ko shugabanni, ko sauran waɗanda za su yi aiki, kome ba.
17 Зато им рекох: Видите у каквом смо злу, Јерусалим пуст и врата му попаљена огњем; дајте да зидамо зидове јерусалимске, да више не будемо руг.
Sai na ce musu, “Kun ga matsalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta da wuta. Ku zo mu sāke gina katangar Urushalima, ba za mu ƙara shan kunya ba.”
18 И казах им како је добра рука Бога мог нада мном и речи цареве које ми је рекао. Тада рекоше: Устанимо и зидајмо. И укрепише им се руке на добро.
Na kuma faɗa musu game da yadda alherin Allahna yake tare da ni da kuma abin da sarki ya faɗa mini. Suka amsa, suka ce, “Mu tashi, mu kama gini.” Sai suka fara wannan aiki mai kyau.
19 А кад то чу Санавалат Ороњанин и Товија, слуга Амонац и Гисем Арапин, подсмеваше нам се и ругаше нам се говорећи: Шта то радите? Да се нећете одметнути цару?
Amma sa’ad da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon da kuma Geshem mutumin Arab suka ji game da wannan, sai suka yi mana ba’a suka kuma yi mana dariya. Suka ce, “Me kuke tsammani kuke yi? Kuna so ku yi wa sarki tawaye ne?”
20 А ја им одговорих и рекох: Бог небески даће нам срећу, а ми, слуге Његове устасмо и зидамо; али ви немате дела ни права ни спомена у Јерусалиму.
Na amsa musu na ce, “Allah na sama zai ba mu nasara. Mu bayinsa za mu tashi mu fara gini, amma game da ku kam, ba ku da rabo cikin Urushalima, ba ku da wani hakki ko wani abin tunawa.”

< Књига Немијина 2 >