< Лука 5 >

1 Једанпут пак, кад народ належе к Њему да слушају реч Божију Он стајаше код језера генисаретског,
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 И виде две лађе где стоје у крају, а рибари беху изишли из њих и испираху мреже:
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 И уђе у једну од лађа која беше Симонова, и замоли га да мало одмакне од краја; и седавши учаше народ из лађе.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 А кад преста говорити, рече Симону: Хајде на дубину, и баците мреже своје те ловите.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 И одговарајући Симон рече Му: Учитељу! Сву ноћ смо се трудили, и ништа не ухватисмо: али по Твојој речи бацићу мрежу.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 И учинивши то ухватише велико мноштво риба, и мреже им се продреше.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 И намагоше на друштво које беше на другој лађи да дођу да им помогну; и дођоше, и напунише обе лађе тако да се готово потопе.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 А кад виде Симон Петар, припаде ка коленима Исусовим говорећи: Изиђи од мене, Господе! Ја сам човек грешан.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Јер беше ушао страх у њега и у све који беху с њим од мноштва риба које ухватише;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 А тако и у Јакова и Јована, синове Зеведејеве, који беху другови Симонови. И рече Исус Симону: Не бој се; одселе ћеш људе ловити.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 И извукавши обе лађе на земљу оставише све, и отидоше за Њим.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 И кад беше Исус у једном граду, и гле, човек сав у губи: и видевши Исуса паде ничице молећи Му се и говорећи: Господе! Ако хоћеш можеш ме очистити.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 И пруживши руку дохвати га се. И рече: Хоћу, очисти се. И одмах губа спаде с њега.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 И Он му заповеди да ником не казује: Него иди и покажи се свештенику, и принеси дар за очишћење своје, како је заповедио Мојсије за сведочанство њима.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Али се глас о Њему још већма разлажаше, и мноштво народа стецаше се да Га слушају и да их исцељује од њихових болести.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 А Он одлажаше у пустињу и мољаше се Богу.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 И један дан учаше Он, и онде сеђаху фарисеји и законици који беху дошли из свију села галилејских и јудејских и из Јерусалима; и сила Господња исцељиваше их.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 И гле, људи донесоше на одру човека који беше узет, и тражаху да га унесу и метну преда Њ;
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 И не нашавши куда ће га унети од народа, попеше се на кућу и кроз кров спустише га с одром на среду пред Исуса.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 И видевши веру њихову рече му: Човече! Опраштају ти се греси твоји.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 И почеше помишљати књижевници и фарисеји говорећи: Ко је овај што хули на Бога? Ко може опраштати грехе осим једног Бога?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 А кад разуме Исус помисли њихове, одговарајући рече им: Шта мислите у срцима својим?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Шта је лакше рећи: Опраштају ти се греси твоји? Или рећи: Устани и ходи?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Него да знате да власт има Син човечији на земљи опраштати грехе, (рече узетоме: ) теби говорим: устани и узми одар свој и иди кући својој.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 И одмах устаде пред њима, и узе на чему лежаше, и отиде кући својој хвалећи Бога.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 И сви се запрепастише, и хваљаху Бога, и напунивши се страха говораху: Чуда се нагледасмо данас!
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 И потом изиђе, и виде цариника по имену Левија где седи на царини, и рече му: Хајде за мном.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 И оставивши све, устаде и пође за Њим.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 И зготови Му Левије код куће своје велику част; и беше много цариника и других који сеђаху с Њим за трпезом.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 И викаху на Њега књижевници и фарисеји говорећи ученицима Његовим: Зашто с цариницима и грешницима једете и пијете?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 И одговарајући Исус рече им: Не требају здрави лекара него болесни.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Ја нисам дошао да дозовем праведнике него грешнике на покајање.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 А они Му рекоше: Зашто ученици Јованови посте често и моле се Богу, тако и фарисејски; а твоји једу и пију?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 А Он им рече: Можете ли сватове натерати да посте док је женик с њима?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Него ће доћи дани кад ће се отети од њих женик, и онда ће постити у оне дане.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Каза им пак и причу: Нико не меће закрпе од нове хаљине на стару хаљину, иначе ће и нову раздрети, и старој не личи шта је од новог.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 И нико не лије вино ново у мехове старе; иначе продре ново вино мехове и оно се пролије, и мехови пропадну;
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Него вино ново у мехове нове треба лити, и обоје ће се сачувати.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 И нико пивши старо неће одмах новог; јер вели: Старо је боље.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Лука 5 >