< Јован 13 >

1 А пред празник пасхе знајући Исус да Му дође час да пређе из овог света к Оцу, како је љубио своје који беху на свету, до краја их љуби.
Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
2 И по вечери, кад већ ђаво беше метнуо у срце Јуди Симонову Искариотском да Га изда,
Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
3 Знајући Исус да Му све Отац даде у руке, и да од Бога изиђе, и к Богу иде,
Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
4 Устаде од вечере, и скиде своје хаљине, и узе убрус те се запреже;
saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
5 Потом усу воду у умиваоницу, и поче прати ноге ученицима и отирати убрусом којим беше запрегнут.
Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
6 Онда дође к Симону Петру, и он Му рече: Господе! Зар Ти моје ноге да опереш?
Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
7 Исус одговори и рече му: Шта ја чиним ти сад не знаш, али ћеш после дознати.
Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
8 Рече Му Петар: Никад Ти нећеш опрати моје ноге. Исус му одговори: Ако те не оперем немаш део са мном. (aiōn g165)
Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn g165)
9 Рече Му Симон Петар: Господе! Не само ноге моје, него и руке и главу.
Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
10 Исус му рече: Опраном не треба до само ноге опрати, јер је сав чист; и ви сте чисти, али не сви.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
11 Јер знаше издајника свог, зато рече: Нисте сви чисти.
Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
12 А кад им опра ноге, узе хаљине своје, и седавши опет за трпезу рече им: Знате ли шта ја учиних вама?
Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
13 Ви зовете мене учитељем и Господом; и право велите: јер јесам.
Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
14 Кад дакле ја опрах вама ноге, Господ и учитељ, и ви сте дужни један другом прати ноге.
Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
15 Јер ја вам дадох углед да и ви тако чините као што ја вама учиних.
Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
16 Заиста, заиста вам кажем: Није слуга већи од господара свог, нити је посланик већи од оног који га је послао.
Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
17 Кад ово знате, благо вама ако га извршујете.
Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
18 Не говорим за све вас, јер ја знам које изабрах; него да се збуде писмо: Који са мном хлеб једе подиже пету своју на ме.
“Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
19 Сад вам кажем пре него се збуде, да кад се збуде, верујете да сам ја.
“Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
20 Заиста, заиста вам кажем: Који прима оног кога пошаљем мене прима; а ко прима мене прима Оног који ме посла.
Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
21 Рекавши ово Исус поста жалостан у духу, и посведочи и рече: Заиста, заиста вам кажем: Један између вас издаће ме.
Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 Онда се ученици згледаху међу собом, и чуђаху се за кога говори.
Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
23 А један од ученика Његових, ког Исус љубљаше, сеђаше за трпезом на крилу Исусовом.
Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
24 Онда намаже на њега Симон Петар да запита ко би то био за кога говори.
Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
25 А он леже на прси Исусове и рече Му: Господе! Ко је то?
Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
26 Исус одговори: Онај је коме ја умочивши залогај дам. И умочивши залогај даде Јуди Симоновом Искариотском.
Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
27 И по залогају тада уђе у њега сотона. Онда му рече Исус: Шта чиниш чини брже.
Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
28 А ово не разуме нико од оних што сеђаху за трпезом зашто му рече.
Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
29 А неки мишљаху, будући да у Јуде беше кеса, да му Исус рече: Купи шта треба за празник; или да да шта сиромашнима.
Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
30 А он узевши залогај одмах изиђе; а беше ноћ.
Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
31 Кад он изиђе, онда Исус рече: Сад се прослави Син човечији и Бог се прослави у Њему.
Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
32 Ако се Бог прослави у Њему, и Бог ће Њега прославити у себи, и одмах ће Га прославити.
In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
33 Дечице! Још сам мало с вама; тражићете ме, и као што рекох Јудејцима: Куда ја идем ви не можете доћи, и вама говорим сад.
“’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
34 Нову вам заповест дајем да љубите један другог, као што ја вас љубих, да се и ви љубите међу собом.
“Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
35 По томе ће сви познати да сте моји ученици, ако будете имали љубав међу собом.
Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
36 Рече Му Симон Петар: Господе! Куда идеш? Исус му одговори: Куда ја идем не можеш сад ићи за мном, али ћеш после поћи за мном.
Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
37 Петар Му рече: Господе! Зашто сад не могу ићи за Тобом? Душу ћу своју положити за Те.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
38 Одговори му Исус: Душу ли ћеш своју положити за ме? Заиста, заиста ти кажем: неће петао запевати док ме се трипут не одрекнеш.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!

< Јован 13 >