< Књига о Јову 2 >

1 Опет један дан дођоше синови Божји да стану пред Господом, а дође и Сотона међу њих да стане пред Господом.
Wata rana kuma mala’iku suka sāke kawo kansu gaban Ubangiji, sai Shaiɗan shi ma ya zo tare da su yă nuna kansa a gabansa.
2 И Господ рече Сотони: Од куда идеш? А Сотона одговори Господу и рече: Проходих земљу и обилазих.
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
3 И рече Господ Сотони: Јеси ли видео слугу мог Јова? Нема онаквог човека на земљи, доброг и праведног, који се боји Бога и уклања се ода зла, и још се држи доброте своје, премда си ме наговорио, те га упропастих низашта.
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah ba ruwansa da mugunta. Kuma har yanzu bai fasa zama mai aminci ba duk da wahalar da ka sa na bari ka ba shi ba tare da wani dalili ba.”
4 А Сотона одговори Господу и рече: Кожа за кожу, и све што човек има даће за душу своју.
Shaiɗan ya amsa ya ce, “Fata don fata! Mutum zai iya rabuwa da duk abin da yake da shi domin ransa.
5 Него пружи руку своју и дотакни се костију његових и меса његовог, псоваће те у очи.
Ka ɗan taɓa lafiyar jikinsa ka gani ba shakka zai la’anta ka kana ji kana gani.”
6 А Господ рече Сотони: Ево ти га у руке; али му душу чувај.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.”
7 И сотона отиде од Господа, и удари Јова злим приштем од пете до темена,
Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji, ya je ya sa wa Ayuba ƙuraje masu zafi a jikinsa daga tafin ƙafafunsa har zuwa kansa.
8 Те он узе цреп па се стругаше, и сеђаше у пепелу.
Sai Ayuba ya ɗauki kaskon tukunya yana ta sosa ƙurajen da shi, yayinda yake zaune cikin toka.
9 И рече му жена: Хоћеш ли се још држати доброте своје? Благослови Бога, па умри.
Matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana nan da amincinka? Ka la’anta Allah ka mutu!”
10 А он јој рече: Говориш као луда жена; добро смо примали од Бога, а зла зар нећемо примати? Уза све то не сагреши Јов уснама својим.
Ya amsa ya ce, “Kina magana kamar wawiya. Alheri kaɗai za mu dinga samu daga Allah ban da wahala?” A cikin wannan duka Ayuba bai yi zunubi ba cikin maganarsa.
11 А три пријатеља Јовова чуше за све зло које га задеси, и дођоше сваки из свог места, Елифас Теманац и Вилдад Сушанин и Софар Намаћанин, договорише се да дођу да га пожале и потеше.
Lokacin da abokan Ayuba su uku wato, Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na’ama suka ji wahalar da ta auka wa Ayuba, sai suka shirya suka bar gidajensu suka je don su ta’azantar da shi.
12 И подигавши очи своје издалека не познаше га; тада подигоше глас свој и стадоше плакати и раздреше сваки свој плашт и посуше се прахом по глави бацајући га у небо.
Sa’ad da suka gan shi daga nesa, da ƙyar suka gane shi; sai suka fara kuka da ƙarfi, suka yayyaga tufafinsu suka zuba toka a kawunansu,
13 И сеђаху код њега на земљи седам дана и седам ноћи, и ниједан му не проговори речи, јер виђаху да је бол врло велик.
sai suka zauna da shi a ƙasa har kwana bakwai. Ba wanda ya ce masa kome, don sun ga tsananin wahalar da yake ciki.

< Књига о Јову 2 >