< Ruta 4 >

1 A Voz izide na vrata gradska, i sjede ondje. I gle, naiðe onaj osvetnik, za kojega Voz govoraše, i reèe mu Voz: hodi ovamo, sjedi ovdje. I on doðe i sjede.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Potom uze Voz deset ljudi izmeðu starješina gradskih i reèe: posjedajte ovdje. I posjedaše.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Tada reèe onomu osvetniku: njivu koja je bila brata našega Elimeleha prodala je Nojemina, koja se vratila iz zemlje Moavske.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 Zato rekoh: da javim tebi, i kažem ti: uzmi njivu pred ovima što sjede ovdje i pred starješinama naroda mojega; ako æeš otkupiti, otkupi; ako li neæeš otkupiti, kaži mi da znam; jer osim tebe nema drugoga koji bi otkupio, a poslije tebe idem ja. A on reèe: ja æu otkupiti.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 A Voz reèe: u koji dan uzmeš njivu iz ruke Nojeminine, treba da uzmeš i Rutu Moavku ženu umrloga, da podigneš ime umrlomu u našljedstvu njegovu.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 Tada reèe onaj osvetnik: ne mogu otkupiti, da ne raspem svojega našljedstva; otkupi ti što bi trebalo da ja otkupim, jer ja ne mogu otkupiti.
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 A bijaše od starine obièaj u Izrailju o otkupljivanju i promijenjivanju, da bi svaka stvar bila tvrda, da jedan izuje obuæu svoju i da drugomu, i to bijaše svedodžba u Izrailju.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 Kad dakle onaj osvetnik reèe Vozu: uzmi ti, izu obuæu svoju.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 A Voz reèe starješinama i svemu narodu: vi ste svjedoci danas da sam otkupio iz ruke Nojeminine što je god bilo Elimelehovo i što je god bilo Heleonovo i Malonovo;
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 I da sam uzeo za ženu Rutu Moavku ženu Malonovu da podignem ime umrlomu u našljedstvu njegovu, da ne bi poginulo ime umrlomu meðu braæom njegovom i u mjestu njegovu; vi ste svjedoci danas.
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 I sav narod koji bijaše na vratima gradskim i starješine rekoše: svjedoci smo; da da Gospod da žena koja dolazi u dom tvoj bude kao Rahilja i Lija, koje obje sazidaše dom Izrailjev; bogati se u Efrati, i proslavi ime svoje u Vitlejemu!
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 I od sjemena koje ti Gospod da od te žene, da postane dom tvoj kao dom Faresa kojega rodi Tamara Judi.
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 I tako uze Voz Rutu i bi mu žena, i on leže s njom, i Gospod joj dade te zatrudnje, i rodi sina.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 I rekoše žene Nojemini: da je blagosloven Gospod koji te nije ostavio danas bez osvetnika, da se ime njegovo slavi u Izrailju!
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 On æe ti utješiti dušu i biæe potpora starosti tvojoj, jer ga rodi snaha tvoja koja te ljubi i koja ti je bolja nego sedam sinova.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 I uze Nojemina dijete, i metnu ga na krilo svoje, i bješe mu dadilja.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 I susjede nadješe mu ime govoreæi: rodi se sin Nojemini, i prozvaše ga Ovid. On bi otac Jeseja oca Davidova.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 A ovo je pleme Faresovo: Fares rodi Esroma;
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 A Esrom rodi Arama; a Aram rodi Aminadava;
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 A Aminadav rodi Nasona; a Nason rodi Salmona;
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 A Salmon rodi Voza; a Voz rodi Ovida;
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 A Ovid rodi Jeseja; a Jesej rodi Davida.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Ruta 4 >