< Luki 5 >

1 Jedanput pak kad narod naleže k njemu da slušaju rijeè Božiju on stajaše kod jezera Genisaretskoga,
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 I vidje dvije laðe gdje stoje u kraju, a ribari bijahu izišli iz njih i ispirahu mreže:
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 I uljeze u jednu od laði koja bješe Simonova, i zamoli ga da malo odmakne od kraja; i sjedavši uèaše narod iz laðe.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 A kad presta govoriti, reèe Simonu: hajde na dubinu, i bacite mreže svoje te lovite.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 I odgovarajuæi Simon reèe mu: uèitelju! svu noæ smo se trudili, i ništa ne uhvatismo: ali po tvojoj rijeèi baciæu mrežu.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 I uèinivši to uhvatiše veliko mnoštvo riba, i mreže im se prodriješe.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 I namagoše na društvo koje bješe na drugoj laði da doðu da im pomognu; i doðoše, i napuniše obje laðe tako da se gotovo potope.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 A kad vidje Simon Petar, pripade ka koljenima Isusovijem govoreæi: iziði od mene, Gospode! ja sam èovjek griješan.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Jer bijaše ušao strah u njega i u sve koji bijahu s njim od mnoštva riba koje uhvatiše;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 A tako i u Jakova i Jovana, sinove Zevedejeve, koji bijahu drugovi Simonovi. I reèe Isus Simonu: ne boj se; otsele æeš ljude loviti.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 I izvukavši obje laðe na zemlju ostaviše sve, i otidoše za njim.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 I kad bješe Isus u jednom gradu, i gle, èovjek sav u gubi: i vidjevši Isusa pade nièice moleæi mu se i govoreæi: Gospode! ako hoæeš možeš me oèistiti.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 I pruživši ruku dohvati ga se, i reèe: hoæu, oèisti se. I odmah guba spade s njega.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 I on mu zapovjedi da nikom ne kazuje: nego idi i pokaži se svešteniku, i prinesi dar za oèišæenje svoje, kako je zapovjedio Mojsije za svjedoèanstvo njima.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Ali se glas o njemu još veæma razlažaše, i mnoštvo naroda stjecaše se da ga slušaju i da ih iscjeljuje od njihovijeh bolesti.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 A on odlažaše u pustinju i moljaše se Bogu.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 I jedan dan uèaše on, i ondje sjeðahu fariseji i zakonici koji bijahu došli iz sviju sela Galilejskijeh i Judejskijeh i iz Jerusalima; i sila Gospodnja iscjeljivaše ih.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 I gle, ljudi donesoše na odru èovjeka koji bješe uzet, i tražahu da ga unesu i metnu preda nj;
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 I ne našavši kuda æe ga unijeti od naroda, popeše se na kuæu i kroz krov spustiše ga s odrom na srijedu pred Isusa.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 I vidjevši vjeru njihovu reèe mu: èovjeèe! opraštaju ti se grijesi tvoji.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 I poèeše pomišljati književnici i fariseji govoreæi: ko je ovaj što huli na Boga? Ko može opraštati grijehe osim jednoga Boga?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 A kad razumje Isus pomisli njihove, odgovarajuæi reèe im: šta mislite u srcima svojijem?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Šta je lakše reæi: opraštaju ti se grijesi tvoji? ili reæi: ustani i hodi?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Nego da znate da vlast ima sin èovjeèij na zemlji opraštati grijehe, reèe uzetome: ) tebi govorim: ustani i uzmi odar svoj i idi kuæi svojoj.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 I odmah ustade pred njima, i uze na èemu ležaše, i otide kuæi svojoj hvaleæi Boga.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 I svi se upropastiše, i hvaljahu Boga, i napunivši se straha govorahu: èuda se nagledasmo danas!
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 I potom iziðe, i vidje carinika po imenu Levija gdje sjedi na carini, i reèe mu: hajde za mnom.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 I ostavivši sve, ustade i poðe za njim.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 I zgotovi mu Levije kod kuæe svoje veliku èast; i bješe mnogo carinika i drugijeh koji sjeðahu s njim za trpezom.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 I vikahu na njega književnici i fariseji govoreæi uèenicima njegovijem: zašto s carinicima i grješnicima jedete i pijete?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 I odgovarajuæi Isus reèe im: ne trebaju zdravi ljekara nego bolesni.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Ja nijesam došao da dozovem pravednike nego grješnike na pokajanje.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 A oni mu rekoše: zašto uèenici Jovanovi poste èesto i mole se Bogu, tako i farisejski; a tvoji jedu i piju?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 A on im reèe: možete li svatove natjerati da poste dok je ženik s njima?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Nego æe doæi dani kad æe se oteti od njih ženik, i onda æe postiti u one dane.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Kaza im pak i prièu: niko ne meæe zakrpe od nove haljine na staru haljinu, inaèe æe i novu razdrijeti, i staroj ne lièi što je od novoga.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 I niko ne ljeva vina novoga u mjehove stare; inaèe prodre novo vino mjehove i ono se prolije, i mjehovi propadnu;
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Nego vino novo u mjehove nove treba ljevati, i oboje æe se saèuvati.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 I niko pivši staro neæe odmah novoga; jer veli: staro je bolje.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luki 5 >