< 2 Kraljevima 13 >

1 Godine dvadeset treæe carovanja Joasa sina Ohozijina nad Judom zacari se Joahaz sin Jujev nad Izrailjem u Samariji, i carova sedamnaest godina.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 I èinjaše što je zlo pred Gospodom, jer hoðaše za grijesima Jerovoama sina Navatova, kojima navede na grijeh Izrailja i ne otstupi od njih.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 Zato se razgnjevi Gospod na Izrailja i dade ih u ruke Azailu caru Sirskom i u ruke Ven-Adadu sinu Azailovu za sve ono vrijeme.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 Ali se Joahaz pomoli Gospodu, i Gospod ga usliši, jer vidje nevolju Izrailjevu, kako ih muèi car Sirski.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 I dade Gospod Izrailju izbavitelja, te se oprostiše ruke Sirske, i življahu sinovi Izrailjevi u šatorima svojim kao prije.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Ali ne otstupiše od grijehova doma Jerovoamova kojima na grijeh navede Izrailja, nego hodiše u njima, i sam lug još stajaše u Samariji.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 A ne osta Joahazu naroda više od pedeset konjika i deset kola i deset tisuæa pješaka; nego ih pobi car Sirski i satr ih, te biše kao prah kad se vrše.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 A ostala djela Joahazova i sve što je èinio, i junaštva njegova, nije li to zapisano u dnevniku careva Izrailjevijeh?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 I poèinu Joahaz kod otaca svojih, i pogreboše ga u Samariji; a na mjesto njegovo zacari se Joas sin njegov.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 Godine trideset sedme carovanja Joasova nad Judom zacari se Joas sin Joahazov nad Izrailjem u Samariji, i carova šesnaest godina.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 I èinjaše što je zlo pred Gospodom, ne otstupi ni od jednoga grijeha Jerovoama sina Navatova, koji navede Izrailja na grijeh, nego u njima hoðaše.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 A ostala djela Joasova, i sve što je èinio, i junaštva njegova, kako je vojevao s Amasijom carem Judinijem, nije li to zapisano u dnevniku careva Izrailjevijeh?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 I poèinu Joas kod otaca svojih, a Jerovoam sjede na prijesto njegov; i pogreboše Joasa u Samariji kod careva Izrailjevijeh.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 A Jelisije razbolje se od bolesti, od koje i umrije; i Joas car Izrailjev doðe k njemu, i plaèuæi pred njim govoraše: oèe moj, oèe moj, kola Izrailjeva i konjici njegovi!
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 A Jelisije mu reèe: uzmi luk i strijele. I on uze luk i strijele.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Tada reèe caru Izrailjevu: nategni luk rukom svojom. I nateže luk rukom svojom. A Jelisije metnu ruke svoje caru na ruke.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 I reèe: otvori prozor s istoka. I otvori, a Jelisije reèe: pusti strijelu. I on pusti strijelu, a Jelisije reèe: strijela izbavljenja Gospodnjega, strijela izbavljenja od Siraca; jer æeš pobiti Sirce u Afeku, i satræeš ih.
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Još reèe: uzmi strijele. I uze, a on reèe caru Izrailjevu: udari u zemlju. I udari tri puta, pa stade.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 Tada se rasrdi na nj èovjek Božji i reèe: da si udario pet puta ili šest puta, tada bi pobio Sirce sasvijem; a sada æeš ih samo tri puta razbiti.
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Potom umrije Jelisije, i pogreboše ga. A druge godine udariše èete Moavske na zemlju.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 I dogodi se kad pogrebavahu nekoga èovjeka, ugledaše èetu i baciše èovjeka u grob Jelisijev; i kad èovjek pade i dotaèe se kostiju Jelisijevih, oživje i usta na noge svoje.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 A Azailo car Sirski muèaše Izrailja svega vijeka Joahazova.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 Ali se Gospodu sažali za njima i smilova se na njih i pogleda na njih zavjeta radi svojega s Avramom, Isakom i Jakovom, i ne htje ih istrijebiti i ne odvrže ih od sebe do sada.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 I umrije Azailo car Sirski, i na njegovo se mjesto zacari Ven-Adad sin njegov.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 A Joas sin Joahazov povrati iz ruke Ven-Adada sina Azailova gradove koje bješe Azailo uzeo ratom Joahazu ocu njegovu; tri puta ga razbi Joas, i povrati gradove Izrailjeve.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kraljevima 13 >