< ลูก: 18 >

1 อปรญฺจ โลไกรกฺลานฺไต รฺนิรนฺตรํ ปฺรารฺถยิตวฺยมฺ อิตฺยาศเยน ยีศุนา ทฺฤษฺฏานฺต เอก: กถิต: ฯ
Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
2 กุตฺรจินฺนคเร กศฺจิตฺ ปฺราฑฺวิวาก อาสีตฺ ส อีศฺวรานฺนาพิเภตฺ มานุษำศฺจ นามนฺยตฯ
Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
3 อถ ตตฺปุรวาสินี กาจิทฺวิธวา ตตฺสมีปเมตฺย วิวาทินา สห มม วิวาทํ ปริษฺกุรฺวฺวิติ นิเวทยามาสฯ
A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
4 ตต: ส ปฺราฑฺวิวาก: กิยทฺทินานิ น ตทงฺคีกฺฤตวานฺ ปศฺจาจฺจิตฺเต จินฺตยามาส, ยทฺยปีศฺวรานฺน พิเภมิ มนุษฺยานปิ น มเนฺย
“An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
5 ตถาเปฺยษา วิธวา มำ กฺลิศฺนาติ ตสฺมาทสฺยา วิวาทํ ปริษฺกริษฺยามิ โนเจตฺ สา สทาคตฺย มำ วฺยคฺรํ กริษฺยติฯ
amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
6 ปศฺจาตฺ ปฺรภุรวททฺ อสาวนฺยายปฺราฑฺวิวาโก ยทาห ตตฺร มโน นิธธฺวํฯ
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
7 อีศฺวรสฺย เย 'ภิรุจิตโลกา ทิวานิศํ ปฺรารฺถยนฺเต ส พหุทินานิ วิลมฺพฺยาปิ เตษำ วิวาทานฺ กึ น ปริษฺกริษฺยติ?
Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
8 ยุษฺมานหํ วทามิ ตฺวรยา ปริษฺกริษฺยติ, กินฺตุ ยทา มนุษฺยปุตฺร อาคมิษฺยติ ตทา ปฺฤถิวฺยำ กิมีทฺฤศํ วิศฺวาสํ ปฺราปฺสฺยติ?
Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
9 เย สฺวานฺ ธารฺมฺมิกานฺ ชฺญาตฺวา ปรานฺ ตุจฺฉีกุรฺวฺวนฺติ เอตาทฺฤคฺภฺย: , กิยทฺภฺย อิมํ ทฺฤษฺฏานฺตํ กถยามาสฯ
Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
10 เอก: ผิรูศฺยปร: กรสญฺจายี ทฺวาวิเมา ปฺรารฺถยิตุํ มนฺทิรํ คเตาฯ
“Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
11 ตโต'เสา ผิรูเศฺยกปารฺเศฺว ติษฺฐนฺ เห อีศฺวร อหมนฺยโลกวตฺ โลฐยิตานฺยายี ปารทาริกศฺจ น ภวามิ อสฺย กรสญฺจายินสฺตุลฺยศฺจ น, ตสฺมาตฺตฺวำ ธนฺยํ วทามิฯ
Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
12 สปฺตสุ ทิเนษุ ทินทฺวยมุปวสามิ สรฺวฺวสมฺปตฺเต รฺทศมำศํ ททามิ จ, เอตตฺกถำ กถยนฺ ปฺรารฺถยามาสฯ
Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
13 กินฺตุ ส กรสญฺจายิ ทูเร ติษฺฐนฺ สฺวรฺคํ ทฺรษฺฏุํ เนจฺฉนฺ วกฺษสิ กราฆาตํ กุรฺวฺวนฺ เห อีศฺวร ปาปิษฺฐํ มำ ทยสฺว, อิตฺถํ ปฺรารฺถยามาสฯ
“Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
14 ยุษฺมานหํ วทามิ, ตโยรฺทฺวโย รฺมเธฺย เกวล: กรสญฺจายี ปุณฺยวตฺเตฺวน คณิโต นิชคฺฤหํ ชคาม, ยโต ย: กศฺจิตฺ สฺวมุนฺนมยติ ส นามยิษฺยเต กินฺตุ ย: กศฺจิตฺ สฺวํ นมยติ ส อุนฺนมยิษฺยเตฯ
“Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
15 อถ ศิศูนำ คาตฺรสฺปรฺศารฺถํ โลกาสฺตานฺ ตสฺย สมีปมานินฺยุ: ศิษฺยาสฺตทฺ ทฺฤษฺฏฺวาเนตฺฤนฺ ตรฺชยามาสุ: ,
Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
16 กินฺตุ ยีศุสฺตานาหูย ชคาท, มนฺนิกฏมฺ อาคนฺตุํ ศิศูนฺ อนุชานีธฺวํ ตำศฺจ มา วารยต; ยต อีศฺวรราชฺยาธิการิณ เอษำ สทฺฤศา: ฯ
Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
17 อหํ ยุษฺมานฺ ยถารฺถํ วทามิ, โย ชน: ศิโศ: สทฺฤโศ ภูตฺวา อีศฺวรราชฺยํ น คฺฤหฺลาติ ส เกนาปิ ปฺรกาเรณ ตตฺ ปฺรเวษฺฏุํ น ศกฺโนติฯ
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
18 อปรมฺ เอโกธิปติสฺตํ ปปฺรจฺฉ, เห ปรมคุโร, อนนฺตายุษ: ปฺราปฺตเย มยา กึ กรฺตฺตวฺยํ? (aiōnios g166)
Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
19 ยีศุรุวาจ, มำ กุต: ปรมํ วทสิ? อีศฺวรํ วินา โกปิ ปรโม น ภวติฯ
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
20 ปรทารานฺ มา คจฺฉ, นรํ มา ชหิ, มา โจรย, มิถฺยาสากฺษฺยํ มา เทหิ, มาตรํ ปิตรญฺจ สํมนฺยสฺว, เอตา ยา อาชฺญา: สนฺติ ตาสฺตฺวํ ชานาสิฯ
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
21 ตทา ส อุวาจ, พาลฺยกาลาตฺ สรฺวฺวา เอตา อาจรามิฯ
Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
22 อิติ กถำ ศฺรุตฺวา ยีศุสฺตมวทตฺ, ตถาปิ ตไวกํ กรฺมฺม นฺยูนมาเสฺต, นิชํ สรฺวฺวสฺวํ วิกฺรีย ทริเทฺรโภฺย วิตร, ตสฺมาตฺ สฺวรฺเค ธนํ ปฺราปฺสฺยสิ; ตต อาคตฺย มมานุคามี ภวฯ
Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
23 กินฺเตฺวตำ กถำ ศฺรุตฺวา โสธิปติ: ศุโศจ, ยตสฺตสฺย พหุธนมาสีตฺฯ
Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
24 ตทา ยีศุสฺตมติโศกานฺวิตํ ทฺฤษฺฏฺวา ชคาท, ธนวตามฺ อีศฺวรราชฺยปฺรเวศ: กีทฺฤคฺ ทุษฺกร: ฯ
Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
25 อีศฺวรราเชฺย ธนิน: ปฺรเวศาตฺ สูเจศฺฉิเทฺรณ มหางฺคสฺย คมนาคมเน สุกเรฯ
Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 โศฺรตาร: ปปฺรจฺฉุสฺตรฺหิ เกน ปริตฺราณํ ปฺราปฺสฺยเต?
Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
27 ส อุกฺตวานฺ, ยนฺ มานุเษณาศกฺยํ ตทฺ อีศฺวเรณ ศกฺยํฯ
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
28 ตทา ปิตร อุวาจ, ปศฺย วยํ สรฺวฺวสฺวํ ปริตฺยชฺย ตว ปศฺจาทฺคามิโน'ภวามฯ
Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
29 ตต: ส อุวาจ, ยุษฺมานหํ ยถารฺถํ วทามิ, อีศฺวรราชฺยารฺถํ คฺฤหํ ปิตเรา ภฺราตฺฤคณํ ชายำ สนฺตานำศฺจ ตฺยกฺตวา
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
30 อิห กาเล ตโต'ธิกํ ปรกาเล 'นนฺตายุศฺจ น ปฺราปฺสฺยติ โลก อีทฺฤศ: โกปิ นาสฺติฯ (aiōn g165, aiōnios g166)
da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 อนนฺตรํ ส ทฺวาทศศิษฺยานาหูย พภาเษ, ปศฺยต วยํ ยิรูศาลมฺนครํ ยาม: , ตสฺมาตฺ มนุษฺยปุเตฺร ภวิษฺยทฺวาทิภิรุกฺตํ ยทสฺติ ตทนุรูปํ ตํ ปฺรติ ฆฏิษฺยเต;
Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
32 วสฺตุตสฺตุ โส'นฺยเทศียานำ หเสฺตษุ สมรฺปยิษฺยเต, เต ตมุปหสิษฺยนฺติ, อนฺยายมาจริษฺยนฺติ ตทฺวปุษิ นิษฺฐีวํ นิกฺเษปฺสฺยนฺติ, กศาภิ: ปฺรหฺฤตฺย ตํ หนิษฺยนฺติ จ,
Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
33 กินฺตุ ตฺฤตียทิเน ส ศฺมศานาทฺ อุตฺถาสฺยติฯ
za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
34 เอตสฺยา: กถายา อภิปฺรายํ กิญฺจิทปิ เต โพทฺธุํ น เศกุ: เตษำ นิกเฏ'สฺปษฺฏตวาตฺ ตไสฺยตาสำ กถานามฺ อาศยํ เต ชฺญาตุํ น เศกุศฺจฯ
Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
35 อถ ตสฺมินฺ ยิรีโห: ปุรสฺยานฺติกํ ปฺราปฺเต กศฺจิทนฺธ: ปถ: ปารฺศฺว อุปวิศฺย ภิกฺษามฺ อกโรตฺ
Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
36 ส โลกสมูหสฺย คมนศพฺทํ ศฺรุตฺวา ตตฺการณํ ปฺฤษฺฏวานฺฯ
Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
37 นาสรตียยีศุรฺยาตีติ โลไกรุกฺเต ส อุจฺไจรฺวกฺตุมาเรเภ,
Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
38 เห ทายูท: สนฺตาน ยีโศ มำ ทยสฺวฯ
Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
39 ตโตคฺรคามินสฺตํ เมานี ติษฺเฐติ ตรฺชยามาสุ: กินฺตุ ส ปุนารุวนฺ อุวาจ, เห ทายูท: สนฺตาน มำ ทยสฺวฯ
Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
40 ตทา ยีศุ: สฺถคิโต ภูตฺวา สฺวานฺติเก ตมาเนตุมฺ อาทิเทศฯ
Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
41 ตต: ส ตสฺยานฺติกมฺ อาคมตฺ, ตทา ส ตํ ปปฺรจฺฉ, ตฺวํ กิมิจฺฉสิ? ตฺวทรฺถมหํ กึ กริษฺยามิ? ส อุกฺตวานฺ, เห ปฺรโภ'หํ ทฺรษฺฏุํ ลไภฯ
“Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
42 ตทา ยีศุรุวาจ, ทฺฤษฺฏิศกฺตึ คฺฤหาณ ตว ปฺรตฺยยสฺตฺวำ สฺวสฺถํ กฺฤตวานฺฯ
Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 ตตสฺตตฺกฺษณาตฺ ตสฺย จกฺษุษี ปฺรสนฺเน; ตสฺมาตฺ ส อีศฺวรํ ธนฺยํ วทนฺ ตตฺปศฺจาทฺ ยเยา, ตทาโลกฺย สรฺเวฺว โลกา อีศฺวรํ ปฺรศํสิตุมฺ อาเรภิเรฯ
Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.

< ลูก: 18 >