< lūkaḥ 8 >

1 aparañca yīśu rdvādaśabhiḥ śiṣyaiḥ sārddhaṁ nānānagareṣu nānāgrāmeṣu ca gacchan iśvarīyarājatvasya susaṁvādaṁ pracārayituṁ prārebhe|
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 tadā yasyāḥ sapta bhūtā niragacchan sā magdalīnīti vikhyātā mariyam herodrājasya gṛhādhipateḥ hoṣe rbhāryyā yohanā śūśānā
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 prabhṛtayo yā bahvyaḥ striyaḥ duṣṭabhūtebhyo rogebhyaśca muktāḥ satyo nijavibhūtī rvyayitvā tamasevanta, tāḥ sarvvāstena sārddham āsan|
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 anantaraṁ nānānagarebhyo bahavo lokā āgatya tasya samīpe'milan, tadā sa tebhya ekāṁ dṛṣṭāntakathāṁ kathayāmāsa| ekaḥ kṛṣībalo bījāni vaptuṁ bahirjagāma,
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 tato vapanakāle katipayāni bījāni mārgapārśve petuḥ, tatastāni padatalai rdalitāni pakṣibhi rbhakṣitāni ca|
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 katipayāni bījāni pāṣāṇasthale patitāni yadyapi tānyaṅkuritāni tathāpi rasābhāvāt śuśuṣuḥ|
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 katipayāni bījāni kaṇṭakivanamadhye patitāni tataḥ kaṇṭakivanāni saṁvṛddhya tāni jagrasuḥ|
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 tadanyāni katipayabījāni ca bhūmyāmuttamāyāṁ petustatastānyaṅkurayitvā śataguṇāni phalāni pheluḥ| sa imā kathāṁ kathayitvā proccaiḥ provāca, yasya śrotuṁ śrotre staḥ sa śṛṇotu|
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 tataḥ paraṁ śiṣyāstaṁ papracchurasya dṛṣṭāntasya kiṁ tātparyyaṁ?
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 tataḥ sa vyājahāra, īśvarīyarājyasya guhyāni jñātuṁ yuṣmabhyamadhikāro dīyate kintvanye yathā dṛṣṭvāpi na paśyanti śrutvāpi ma budhyante ca tadarthaṁ teṣāṁ purastāt tāḥ sarvvāḥ kathā dṛṣṭāntena kathyante|
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 dṛṣṭāntasyāsyābhiprāyaḥ, īśvarīyakathā bījasvarūpā|
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 ye kathāmātraṁ śṛṇvanti kintu paścād viśvasya yathā paritrāṇaṁ na prāpnuvanti tadāśayena śaitānetya hṛdayātṛ tāṁ kathām apaharati ta eva mārgapārśvasthabhūmisvarūpāḥ|
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 ye kathaṁ śrutvā sānandaṁ gṛhlanti kintvabaddhamūlatvāt svalpakālamātraṁ pratītya parīkṣākāle bhraśyanti taeva pāṣāṇabhūmisvarūpāḥ|
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 ye kathāṁ śrutvā yānti viṣayacintāyāṁ dhanalobhena ehikasukhe ca majjanta upayuktaphalāni na phalanti ta evoptabījakaṇṭakibhūsvarūpāḥ|
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 kintu ye śrutvā saralaiḥ śuddhaiścāntaḥkaraṇaiḥ kathāṁ gṛhlanti dhairyyam avalambya phalānyutpādayanti ca ta evottamamṛtsvarūpāḥ|
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 aparañca pradīpaṁ prajvālya kopi pātreṇa nācchādayati tathā khaṭvādhopi na sthāpayati, kintu dīpādhāroparyyeva sthāpayati, tasmāt praveśakā dīptiṁ paśyanti|
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 yanna prakāśayiṣyate tādṛg aprakāśitaṁ vastu kimapi nāsti yacca na suvyaktaṁ pracārayiṣyate tādṛg gṛptaṁ vastu kimapi nāsti|
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 ato yūyaṁ kena prakāreṇa śṛṇutha tatra sāvadhānā bhavata, yasya samīpe barddhate tasmai punardāsyate kintu yasyāśraye na barddhate tasya yadyadasti tadapi tasmāt neṣyate|
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 aparañca yīśo rmātā bhrātaraśca tasya samīpaṁ jigamiṣavaḥ
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 kintu janatāsambādhāt tatsannidhiṁ prāptuṁ na śekuḥ| tatpaścāt tava mātā bhrātaraśca tvāṁ sākṣāt cikīrṣanto bahistiṣṭhanatīti vārttāyāṁ tasmai kathitāyāṁ
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 sa pratyuvāca; ye janā īśvarasya kathāṁ śrutvā tadanurūpamācaranti taeva mama mātā bhrātaraśca|
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 anantaraṁ ekadā yīśuḥ śiṣyaiḥ sārddhaṁ nāvamāruhya jagāda, āyāta vayaṁ hradasya pāraṁ yāmaḥ, tataste jagmuḥ|
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 teṣu naukāṁ vāhayatsu sa nidadrau;
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 athākasmāt prabalajhañbhśagamād hrade naukāyāṁ taraṅgairācchannāyāṁ vipat tān jagrāsa|tasmād yīśorantikaṁ gatvā he guro he guro prāṇā no yāntīti gaditvā taṁ jāgarayāmbabhūvuḥ|tadā sa utthāya vāyuṁ taraṅgāṁśca tarjayāmāsa tasmādubhau nivṛtya sthirau babhūvatuḥ|
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 sa tān babhāṣe yuṣmākaṁ viśvāsaḥ ka? tasmātte bhītā vismitāśca parasparaṁ jagaduḥ, aho kīdṛgayaṁ manujaḥ pavanaṁ pānīyañcādiśati tadubhayaṁ tadādeśaṁ vahati|
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 tataḥ paraṁ gālīlpradeśasya sammukhasthagiderīyapradeśe naukāyāṁ lagantyāṁ taṭe'varohamāvād
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 bahutithakālaṁ bhūtagrasta eko mānuṣaḥ purādāgatya taṁ sākṣāccakāra| sa manuṣo vāso na paridadhat gṛhe ca na vasan kevalaṁ śmaśānam adhyuvāsa|
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 sa yīśuṁ dṛṣṭvaiva cīcchabdaṁ cakāra tasya sammukhe patitvā proccairjagāda ca, he sarvvapradhāneśvarasya putra, mayā saha tava kaḥ sambandhaḥ? tvayi vinayaṁ karomi māṁ mā yātaya|
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 yataḥ sa taṁ mānuṣaṁ tyaktvā yātum amedhyabhūtam ādideśa; sa bhūtastaṁ mānuṣam asakṛd dadhāra tasmāllokāḥ śṛṅkhalena nigaḍena ca babandhuḥ; sa tad bhaṁktvā bhūtavaśatvāt madhyeprāntaraṁ yayau|
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 anantaraṁ yīśustaṁ papraccha tava kinnāma? sa uvāca, mama nāma bāhino yato bahavo bhūtāstamāśiśriyuḥ|
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 atha bhūtā vinayena jagaduḥ, gabhīraṁ garttaṁ gantuṁ mājñāpayāsmān| (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 tadā parvvatopari varāhavrajaścarati tasmād bhūtā vinayena procuḥ, amuṁ varāhavrajam āśrayitum asmān anujānīhi; tataḥ sonujajñau|
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 tataḥ paraṁ bhūtāstaṁ mānuṣaṁ vihāya varāhavrajam āśiśriyuḥ varāhavrajāśca tatkṣaṇāt kaṭakena dhāvanto hrade prāṇān vijṛhuḥ|
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 tad dṛṣṭvā śūkararakṣakāḥ palāyamānā nagaraṁ grāmañca gatvā tatsarvvavṛttāntaṁ kathayāmāsuḥ|
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 tataḥ kiṁ vṛttam etaddarśanārthaṁ lokā nirgatya yīśoḥ samīpaṁ yayuḥ, taṁ mānuṣaṁ tyaktabhūtaṁ parihitavastraṁ svasthamānuṣavad yīśoścaraṇasannidhau sūpaviśantaṁ vilokya bibhyuḥ|
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 ye lokāstasya bhūtagrastasya svāsthyakaraṇaṁ dadṛśuste tebhyaḥ sarvvavṛttāntaṁ kathayāmāsuḥ|
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 tadanantaraṁ tasya giderīyapradeśasya caturdiksthā bahavo janā atitrastā vinayena taṁ jagaduḥ, bhavān asmākaṁ nikaṭād vrajatu tasmāt sa nāvamāruhya tato vyāghuṭya jagāma|
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 tadānīṁ tyaktabhūtamanujastena saha sthātuṁ prārthayāñcakre
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 kintu tadartham īśvaraḥ kīdṛṅmahākarmma kṛtavān iti niveśanaṁ gatvā vijñāpaya, yīśuḥ kathāmetāṁ kathayitvā taṁ visasarja| tataḥ sa vrajitvā yīśustadarthaṁ yanmahākarmma cakāra tat purasya sarvvatra prakāśayituṁ prārebhe|
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 atha yīśau parāvṛtyāgate lokāstaṁ ādareṇa jagṛhu ryasmātte sarvve tamapekṣāñcakrire|
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 tadanantaraṁ yāyīrnāmno bhajanagehasyaikodhipa āgatya yīśoścaraṇayoḥ patitvā svaniveśanāgamanārthaṁ tasmin vinayaṁ cakāra,
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 yatastasya dvādaśavarṣavayaskā kanyaikāsīt sā mṛtakalpābhavat| tatastasya gamanakāle mārge lokānāṁ mahān samāgamo babhūva|
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 dvādaśavarṣāṇi pradararogagrastā nānā vaidyaiścikitsitā sarvvasvaṁ vyayitvāpi svāsthyaṁ na prāptā yā yoṣit sā yīśoḥ paścādāgatya tasya vastragranthiṁ pasparśa|
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 tasmāt tatkṣaṇāt tasyā raktasrāvo ruddhaḥ|
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 tadānīṁ yīśuravadat kenāhaṁ spṛṣṭaḥ? tato'nekairanaṅgīkṛte pitarastasya saṅginaścāvadan, he guro lokā nikaṭasthāḥ santastava dehe gharṣayanti, tathāpi kenāhaṁ spṛṣṭa̮iti bhavān kutaḥ pṛcchati?
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 yīśuḥ kathayāmāsa, kenāpyahaṁ spṛṣṭo, yato mattaḥ śakti rnirgateti mayā niścitamajñāyi|
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 tadā sā nārī svayaṁ na gupteti viditvā kampamānā satī tasya sammukhe papāta; yena nimittena taṁ pasparśa sparśamātrācca yena prakāreṇa svasthābhavat tat sarvvaṁ tasya sākṣādācakhyau|
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 tataḥ sa tāṁ jagāda he kanye susthirā bhava, tava viśvāsastvāṁ svasthām akārṣīt tvaṁ kṣemeṇa yāhi|
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 yīśoretadvākyavadanakāle tasyādhipate rniveśanāt kaścilloka āgatya taṁ babhāṣe, tava kanyā mṛtā guruṁ mā kliśāna|
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 kintu yīśustadākarṇyādhipatiṁ vyājahāra, mā bhaiṣīḥ kevalaṁ viśvasihi tasmāt sā jīviṣyati|
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 atha tasya niveśane prāpte sa pitaraṁ yohanaṁ yākūbañca kanyāyā mātaraṁ pitarañca vinā, anyaṁ kañcana praveṣṭuṁ vārayāmāsa|
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 aparañca ye rudanti vilapanti ca tān sarvvān janān uvāca, yūyaṁ mā rodiṣṭa kanyā na mṛtā nidrāti|
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 kintu sā niścitaṁ mṛteti jñātvā te tamupajahasuḥ|
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 paścāt sa sarvvān bahiḥ kṛtvā kanyāyāḥ karau dhṛtvājuhuve, he kanye tvamuttiṣṭha,
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 tasmāt tasyāḥ prāṇeṣu punarāgateṣu sā tatkṣaṇād uttasyau| tadānīṁ tasyai kiñcid bhakṣyaṁ dātum ādideśa|
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 tatastasyāḥ pitarau vismayaṁ gatau kintu sa tāvādideśa ghaṭanāyā etasyāḥ kathāṁ kasmaicidapi mā kathayataṁ|
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< lūkaḥ 8 >