< lUkaH 1 >

1 prathamato ye sAkSiNo vAkyapracArakAzcAsan te'smAkaM madhye yadyat sapramANaM vAkyamarpayanti sma
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 tadanusArato'nyepi bahavastadvRttAntaM racayituM pravRttAH|
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 ataeva he mahAmahimathiyaphil tvaM yA yAH kathA azikSyathAstAsAM dRDhapramANAni yathA prApnoSi
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 tadarthaM prathamamArabhya tAni sarvvANi jJAtvAhamapi anukramAt sarvvavRttAntAn tubhyaM lekhituM matimakArSam|
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 yihUdAdezIyaherodnAmake rAjatvaM kurvvati abIyayAjakasya paryyAyAdhikArI sikhariyanAmaka eko yAjako hAroNavaMzodbhavA ilIzevAkhyA
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 tasya jAyA dvAvimau nirdoSau prabhoH sarvvAjJA vyavasthAzca saMmanya IzvaradRSTau dhArmmikAvAstAm|
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 tayoH santAna ekopi nAsIt, yata ilIzevA bandhyA tau dvAveva vRddhAvabhavatAm|
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 yadA svaparyyAnukrameNa sikhariya IzvAsya samakSaM yAjakIyaM karmma karoti
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 tadA yajJasya dinaparipAyyA paramezvarasya mandire pravezakAle dhUpajvAlanaM karmma tasya karaNIyamAsIt|
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 taddhUpajvAlanakAle lokanivahe prArthanAM kartuM bahistiSThati
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 sati sikhariyo yasyAM vedyAM dhUpaM jvAlayati taddakSiNapArzve paramezvarasya dUta eka upasthito darzanaM dadau|
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 taM dRSTvA sikhariya udvivije zazaGke ca|
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 tadA sa dUtastaM babhASe he sikhariya mA bhaistava prArthanA grAhyA jAtA tava bhAryyA ilIzevA putraM prasoSyate tasya nAma yohan iti kariSyasi|
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 kiJca tvaM sAnandaH saharSazca bhaviSyasi tasya janmani bahava AnandiSyanti ca|
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 yato hetoH sa paramezvarasya gocare mahAn bhaviSyati tathA drAkSArasaM surAM vA kimapi na pAsyati, aparaM janmArabhya pavitreNAtmanA paripUrNaH
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 san isrAyelvaMzIyAn anekAn prabhoH paramezvarasya mArgamAneSyati|
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 santAnAn prati pitRNAM manAMsi dharmmajJAnaM pratyanAjJAgrAhiNazca parAvarttayituM, prabhoH paramezvarasya sevArtham ekAM sajjitajAtiM vidhAtuJca sa eliyarUpAtmazaktiprAptastasyAgre gamiSyati|
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 tadA sikhariyo dUtamavAdIt kathametad vetsyAmi? yatohaM vRddho mama bhAryyA ca vRddhA|
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 tato dUtaH pratyuvAca pazyezvarasya sAkSAdvarttI jibrAyelnAmA dUtohaM tvayA saha kathAM gadituM tubhyamimAM zubhavArttAM dAtuJca preSitaH|
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 kintu madIyaM vAkyaM kAle phaliSyati tat tvayA na pratItam ataH kAraNAd yAvadeva tAni na setsyanti tAvat tvaM vaktuMmazakto mUko bhava|
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 tadAnIM ye ye lokAH sikhariyamapaikSanta te madhyemandiraM tasya bahuvilambAd AzcaryyaM menire|
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 sa bahirAgato yadA kimapi vAkyaM vaktumazaktaH saGketaM kRtvA niHzabdastasyau tadA madhyemandiraM kasyacid darzanaM tena prAptam iti sarvve bubudhire|
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 anantaraM tasya sevanaparyyAye sampUrNe sati sa nijagehaM jagAma|
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 katipayadineSu gateSu tasya bhAryyA ilIzevA garbbhavatI babhUva
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 pazcAt sA paJcamAsAn saMgopyAkathayat lokAnAM samakSaM mamApamAnaM khaNDayituM paramezvaro mayi dRSTiM pAtayitvA karmmedRzaM kRtavAn|
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 aparaJca tasyA garbbhasya SaSThe mAse jAte gAlIlpradezIyanAsaratpure
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 dAyUdo vaMzIyAya yUSaphnAmne puruSAya yA mariyamnAmakumArI vAgdattAsIt tasyAH samIpaM jibrAyel dUta IzvareNa prahitaH|
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 sa gatvA jagAda he IzvarAnugRhItakanye tava zubhaM bhUyAt prabhuH paramezvarastava sahAyosti nArINAM madhye tvameva dhanyA|
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 tadAnIM sA taM dRSTvA tasya vAkyata udvijya kIdRzaM bhASaNamidam iti manasA cintayAmAsa|
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 tato dUto'vadat he mariyam bhayaM mAkArSIH, tvayi paramezvarasyAnugrahosti|
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 pazya tvaM garbbhaM dhRtvA putraM prasoSyase tasya nAma yIzuriti kariSyasi|
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 sa mahAn bhaviSyati tathA sarvvebhyaH zreSThasya putra iti khyAsyati; aparaM prabhuH paramezvarastasya piturdAyUdaH siMhAsanaM tasmai dAsyati;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 tathA sa yAkUbo vaMzopari sarvvadA rAjatvaM kariSyati, tasya rAjatvasyAnto na bhaviSyati| (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 tadA mariyam taM dUtaM babhASe nAhaM puruSasaGgaM karomi tarhi kathametat sambhaviSyati?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 tato dUto'kathayat pavitra AtmA tvAmAzrAyiSyati tathA sarvvazreSThasya zaktistavopari chAyAM kariSyati tato hetostava garbbhAd yaH pavitrabAlako janiSyate sa Izvaraputra iti khyAtiM prApsyati|
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 aparaJca pazya tava jJAtirilIzevA yAM sarvve bandhyAmavadan idAnIM sA vArddhakye santAnamekaM garbbhe'dhArayat tasya SaSThamAsobhUt|
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 kimapi karmma nAsAdhyam Izvarasya|
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 tadA mariyam jagAda, pazya prabherahaM dAsI mahyaM tava vAkyAnusAreNa sarvvametad ghaTatAm; ananataraM dUtastasyAH samIpAt pratasthe|
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 atha katipayadinAt paraM mariyam tasmAt parvvatamayapradezIyayihUdAyA nagaramekaM zIghraM gatvA
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 sikhariyayAjakasya gRhaM pravizya tasya jAyAm ilIzevAM sambodhyAvadat|
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 tato mariyamaH sambodhanavAkye ilIzevAyAH karNayoH praviSTamAtre sati tasyA garbbhasthabAlako nanartta| tata ilIzevA pavitreNAtmanA paripUrNA satI
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 proccairgaditumArebhe, yoSitAM madhye tvameva dhanyA, tava garbbhasthaH zizuzca dhanyaH|
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 tvaM prabhormAtA, mama nivezane tvayA caraNAvarpitau, mamAdya saubhAgyametat|
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 pazya tava vAkye mama karNayoH praviSTamAtre sati mamodarasthaH zizurAnandAn nanartta|
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 yA strI vyazvasIt sA dhanyA, yato hetostAM prati paramezvaroktaM vAkyaM sarvvaM siddhaM bhaviSyati|
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 tadAnIM mariyam jagAda| dhanyavAdaM parezasya karoti mAmakaM manaH|
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 mamAtmA tArakeze ca samullAsaM pragacchati|
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 akarot sa prabhu rduSTiM svadAsyA durgatiM prati| pazyAdyArabhya mAM dhanyAM vakSyanti puruSAH sadA|
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 yaH sarvvazaktimAn yasya nAmApi ca pavitrakaM| sa eva sumahatkarmma kRtavAn mannimittakaM|
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 ye bibhyati janAstasmAt teSAM santAnapaMktiSu| anukampA tadIyA ca sarvvadaiva sutiSThati|
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 svabAhubalatastena prAkAzyata parAkramaH| manaHkumantraNAsArddhaM vikIryyante'bhimAninaH|
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 siMhAsanagatAllokAn balinazcAvarohya saH| padeSUcceSu lokAMstu kSudrAn saMsthApayatyapi|
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 kSudhitAn mAnavAn dravyairuttamaiH paritarpya saH| sakalAn dhanino lokAn visRjed riktahastakAn|
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 ibrAhImi ca tadvaMze yA dayAsti sadaiva tAM| smRtvA purA pitRNAM no yathA sAkSAt pratizrutaM| (aiōn g165)
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 isrAyelsevakastena tathopakriyate svayaM||
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 anantaraM mariyam prAyeNa mAsatrayam ilIzevayA sahoSitvA vyAghuyya nijanivezanaM yayau|
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 tadanantaram ilIzevAyAH prasavakAla upasthite sati sA putraM prAsoSTa|
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 tataH paramezvarastasyAM mahAnugrahaM kRtavAn etat zrutvA samIpavAsinaH kuTumbAzcAgatya tayA saha mumudire|
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 tathASTame dine te bAlakasya tvacaM chettum etya tasya pitRnAmAnurUpaM tannAma sikhariya iti karttumISuH|
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 kintu tasya mAtAkathayat tanna, nAmAsya yohan iti karttavyam|
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 tadA te vyAharan tava vaMzamadhye nAmedRzaM kasyApi nAsti|
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 tataH paraM tasya pitaraM sikhariyaM prati saGketya papracchuH zizoH kiM nAma kAriSyate?
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 tataH sa phalakamekaM yAcitvA lilekha tasya nAma yohan bhaviSyati| tasmAt sarvve AzcaryyaM menire|
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 tatkSaNaM sikhariyasya jihvAjADye'pagate sa mukhaM vyAdAya spaSTavarNamuccAryya Izvarasya guNAnuvAdaM cakAra|
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 tasmAccaturdiksthAH samIpavAsilokA bhItA evametAH sarvvAH kathA yihUdAyAH parvvatamayapradezasya sarvvatra pracAritAH|
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 tasmAt zrotAro manaHsu sthApayitvA kathayAmbabhUvuH kIdRzoyaM bAlo bhaviSyati? atha paramezvarastasya sahAyobhUt|
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 tadA yohanaH pitA sikhariyaH pavitreNAtmanA paripUrNaH san etAdRzaM bhaviSyadvAkyaM kathayAmAsa|
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 isrAyelaH prabhu ryastu sa dhanyaH paramezvaraH| anugRhya nijAllokAn sa eva parimocayet|
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 vipakSajanahastebhyo yathA mocyAmahe vayaM| yAvajjIvaJca dharmmeNa sAralyena ca nirbhayAH|
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 sevAmahai tamevaikam etatkAraNameva ca| svakIyaM supavitraJca saMsmRtya niyamaM sadA|
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 kRpayA puruSAn pUrvvAn nikaSArthAttu naH pituH| ibrAhImaH samIpe yaM zapathaM kRtavAn purA|
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 tameva saphalaM karttaM tathA zatrugaNasya ca| RtIyAkAriNazcaiva karebhyo rakSaNAya naH|
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 sRSTeH prathamataH svIyaiH pavitrai rbhAvivAdibhiH| (aiōn g165)
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 yathoktavAn tathA svasya dAyUdaH sevakasya tu|
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 vaMze trAtAramekaM sa samutpAditavAn svayam|
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 ato he bAlaka tvantu sarvvebhyaH zreSTha eva yaH| tasyaiva bhAvivAdIti pravikhyAto bhaviSyasi| asmAkaM caraNAn kSeme mArge cAlayituM sadA| evaM dhvAnte'rthato mRtyozchAyAyAM ye tu mAnavAH|
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 upaviSTAstu tAneva prakAzayitumeva hi| kRtvA mahAnukampAM hi yAmeva paramezvaraH|
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 UrdvvAt sUryyamudAyyaivAsmabhyaM prAdAttu darzanaM| tayAnukampayA svasya lokAnAM pApamocane|
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 paritrANasya tebhyo hi jJAnavizrANanAya ca| prabho rmArgaM pariSkarttuM tasyAgrAyI bhaviSyasi||
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 atha bAlakaH zarIreNa buddhyA ca varddhitumArebhe; aparaJca sa isrAyelo vaMzIyalokAnAM samIpe yAvanna prakaTIbhUtastAstAvat prAntare nyavasat|
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< lUkaH 1 >