< Luke 8 >

1 Hanchu, môrkhat suole chu, Jisua'n Galilee ram khopuingei le khuongei nâma Pathien Rêngram Thurchi Sa misîrin a chaia. Ruoisi sômleinik ngeiin an jûia.
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 Nupang senkhat ramkhori sûr renga an natnangeia a dam, Mary Magdalene, a sûng renga ramkhori sari a rujûlpai pe,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 Herod office'a sin milien Chuza lômnu Joanna ngei, Susanna ngei, le midang nupang tamtak ngeiin an jûi saa. Hi mingei hin an sumin Jisua le a ruoisingei an san ngei ngâi ani.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Khopui ankhat renga adanga mipuingei Jisua kôm an hong intûpkhôma, Jisua'n chongmintêkin a ril ngeia.
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 Mi inkhat a bu rît rangin a loilâia a sea. Sachi a rethea, senkhat lampui kôla achula, vangeiin an sâk ripa.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Senkhat lungpherpha pil chunga achula, a hong mônga, pil an zit loi sikin a rôp nôk ripa.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Senkhat chu riling kâra achula, ahong thuora, rilingin adîp thata.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 Senkhat chu pil sana achula, a hong insôna, abâk raza chitin an hong inra zoi. Hanchu hi chongngei hih a rila, Jisua'n, Kuor nin dônin chu rangâi roi, a tipe ngeia.
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 A ruoisingeiin hi chongmintêk omtie, Jisua an rekela.
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 Jisua'n, “Pathien Rêngram chong inthup riettheina nin kôma ipêk ani. Ania midangngei rangin chu, an ena an mu loina rang le an rangâia an rietminthâr loina rangin, chongmintêk vaiin misîr pe rang ani” tiin a thuon ngeia.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 “Chongmintêk omtie chu hi anghin ani; Sachi chu Pathien chong ani.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 Sachi lampui kôla chul chu, chong chu an rieta, ania, an iem loina rang le minringa an om loina rangin Soitanin an chong riet hah an mulungrîl renga a lâk pe ngâia.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Lung chung pila chul chu, an chong riet râisân takin an poma, nikhomrese, an nia han rujung inthuk nei loiin, an chunga minsinna a hongtung tena chu an inlet nôk ngâia.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Riling kâra chul chu, chong an rieta, aniatachu, hi ringnun hoiinhâina le inchongna ngei hin lungkâng a pêka, adîpa, amara reng min phâk ngâi mak.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Pil sana chul chu, chong an riet hah mulungrîla asadimin an dara, an jôma, an inra mâka dier ngei hah anni” a tia.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Tutên châti mochokin bêl nuoia dar ngâi mak ngei, jâlmun nuoia khom dar ngâi mak ngei. A lût murdi'n an mu theina rangin a darna muna kêng an dar ngâi.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Ânthup murdi khom tâng minsuok nîng a ta, ihîpa om murdi khom avâra la minlangsuok nîng atih.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 “Singthei roi, inmo nin rangâi, asikchu, a dônngei chu bôkpe sa nîng a ta, a dônloi chu a dôn vieta ai mindon te ha khom la lâk pe rip an tih,” a tia.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Hanchu, a nû le a lâibungngei Jisua kôma an honga, ania mipui sikin a kôma tung thei mak ngeia.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 Mi inkhatin, “Na nû le na lâibungngeiin nang mu nuomin pêntieng an inding” a tipea.
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 Hanchu, Jisua'n an kôma, “Ka nû le ka lâibungngei chu Pathien chong rangâia a jômngei hih anni” a tia.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Sûnkhat chu Jisua le a ruoisingei rukuonga an chuonga, “Dîl râl tieng son lenkân rei u” a tia, hanchu an inphêta.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 Hanchu an se lâiin, Jisua chu a ina. Inningloiin phâivuopui a hong thoa, an rukuong tuiin a sip vavânga, rolo innîkin an oma.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Hanchu, ruoisingei Jisua kôma an sea, an kaithoia, “Minchupu, Minchupu! Kin thi suo rang kêng ani zoi” an tia. Hanchu, Jisua ânthoia, Phâivuopui le tuidârinsok hah chong a pêka, an dâiruom zoia.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 Hanchu, a ruoisingei kôma, “Khonmo, nan taksônna a om?” a tipe ngeia. Kamâmin an chia, Khoi anga miriem mo hi? Phâivuopui le tuidârinsokngei khom chong a pêka a chong an ijôm hi, anin tia.
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Hanchu Jisua le a ruoisingei hah Galilee dîl râl, Gerasa, ram an tunga.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Jisua'n tuipânga a lôn lehan, khopui renga mi inkhat, ramkhori sûr ân tongpuia. Ha mi hah zora sôttak renga, dierboiin, ina khom om ngâi loiin thâna lei om ngâi ania.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Jisua a mûn chu ânieka, a ke bula ânboka, ânring takin, Jisua Pathien Ânchungtak Nâipasal, imo ni lo rang ni ti? Dûk ni mintong no roh, tiin a ngêna.
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 Jisua'n ratha innim hah chong a pêk sika ma angtaka ai ti ani. Vêl tamtak an sûra, lung ina an khum ngâia, a kut le a ke zingjirûiin an khita chu a potsata, ramkhori han ramchâr tieng han a rujûl ngâi ani.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Jisua'n, “Imo ni riming?” tiin a rekela, “Ki riming chu, Mob” tiin a thuona, a sûnga ramkhori tamtak an lût sikin.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 Hanchu, ramkhoringei han, khurmongboia tîr loina rangin Jisua an ngêna. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Hanchu, ha muol panga han vok pâl sâk rokin an oma, ramkhoringeiin ha vokngei sûnga lût rangin Jisua an ngêna, a phalpe ngeia.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Mipa sûng renga an jôka, vokngei sûnga an lût zoia. Rôlsôr dîl rakhama an tâna, tuia an tâka an thi let zoi.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 Hanchu, vok avâipungei han neinun omtie an rietin chu, an sea khopuia le loia mingei an va ril ngeia.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Hanchu, neinun omtie en rangin mingei an suoka, Jisua kôm an hongin chu, ramkhori sûrpu hah, puon silin, ruthuok kipin Jisua ke bula insungin an mua, an rêngin an chia.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Hanchu, amu nâmin a dam tie mingei kôma an rila,
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Ha Gerasa rama mingei han an chi sikin Jisua hah an kôm renga rot rangin an ngêna, hanchu Jisua rukuonga a chuonga a mâk ngei zoi.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Ramkhori a sûng renga a jôka a dampu han, Jisua kôm nang jûi ki tih, a tia.
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 Hanniresea, Jisua'n, “Ni ina senla, nu chunga Pathien sintho tie va misîr roh” a tipea. Hanchu, a sea, khopui sûng pumpuia a chunga Jisua sintho tie hah a misîr zoi.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Hanchu, Jisua dîl râl tieng a hongtung nôkin chu, mipuingei ama lei ngak sikin an lei modôma.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 Ha khuoa synagog ruoipu Jairus a honga, Jisua ke bula ânboka, a ina se rangin a ngêna.
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 A nâikhât nâinupang, kum sômleinik mi, a thi vavâng sikin. Hanchu, Jisua a sên chu mipuingeiin an ûmhura.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Nupang inkhat kum sômleinik piel, hulloi inrik a oma, ai dôn murdi doctora a thâm let zoia, tute lakin mindam thei mak ngeia.
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 Mipuingei kâra Jisua nûktieng a honga, a puonmor a tôna, harenghan a dam kelena.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 Jisua'n, “Tumo ni tôn?” a tia. Kei chu ni mu-ung an ti chita. Hanchu Peter'n a kôma, “Minchupu, hi dôra mipuiin nang an uop hite” a tipea.
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 Ania, Jisua'n “tuminin chu min tôn, Keima renga sinthotheina ajôk” a tia.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 Nupangnu ani ti rietsuok ani zoi, ti ânriet tena chu, innîk pumin mipuingei makunga, Jisua ke bula inbokin, a tôna harenghan a dam kelen roi hah misîr zoi.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Hanchu, Jisua'n a kôma, “Ka nâinupang, na taksônnân nang a mindam zoi, rathanngam takin se ta roh” a tipea.
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 Jisua'n ha a ti lâitakin, ruoipu in renga thangthei a honga, Jairus kôma, “Na nâinupang a thi zoi, Minchupu jêl khâi no roh” a tia.
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Jisua'n a rieta, Jairus kôma, “Chino roh, iem ngit roh, dam a tih,” a tipea.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 In ava tungin chu Peter, John, Jacob, nâite nû le pa pêna chu tute dang a kôma lût phal maka.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Hataka om murdi nâite chûlin an chapa, Jisua'n, “Chap no roi, athi ni mak, a in kêng” a tia.
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 Hanchu, nâite hah a thi ani iti an riet sikin an munuisana.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 Hanchu, Jisua'n a kut a sûra, “Ka nâite, hong inthoi roh” a tia.
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Hanchu, a ringna a juong kîra, harenghan a hon thoia, Jisua'n “sâk rang imokhat pêk roi” a tia.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 A nû le a pa'n kamâm om an ti tataka; nikhomrese, Jisua'n chu a sintho hah tute ril loi rangin chong a pêka zoi.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >