< Luka 1 >

1 Afwanaje abhantu abhinji bhabheshela amakhono asebhe eshe tukalibu owe nongwa nelwe mombia gula gagu timiziwe pahati yetu,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Neshe bhala shubhatihudithiga bhala bhabhahali bhashahidi bhagalolaga. na bhula atumishi abhalila izu elyufume ahwande.
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Endolile shinza ane nane, afwanaje ehwiyanzie ulwilyoli amambo ega gonti afume huwandilo husimbire hupanjililo Theafilo hwutukfu.
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Opate amanye elyoli emambo gala gohasambelezewe.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Umwaha gwa Herode, umwene uwa Yudea, palino kohani omo itawa lyakwe Zakaria, uwa tandilane no Abya. No she wakwe bhulibhabhebho ya Haruni, itawa lyakwe Elizabeti.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Na hwonti bhabhele bhali bhelyoli hwitagalila elya NGOLOBHE; bhahendeleye ne ndajizwo zwonti ezwa gosi ne ndajizwo lyakwe bila eyaune.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Bhape sebhali no mwana eshi Elizabethi ali gomba, na bhonti bhabhule bhali bhagogolo tee.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Basi nashi nabhombaga embombo eye ukuhani uwa taratibu uwa tandilane hwakwe hwitagalila elyu NGOLOBHE.
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Neshe shashahali ekawaida yao eye Ukuhani, ekora ehangweleye ahwinjile mshibhanza esha gosi ili kufukizo uvumba.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Na mabungano gonti ega bhantu bhali puta hwonze esaa ya kufukiza uvumba.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Wafumilya no malaika uwa gosi ayemeleye upani uwendelo paluputo ya kufukiza.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zakaria nawalola adhugumiye owoga wamwinjiye.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Lelo ula umalaika wabhola uganje, “Awogope Zakaria, eshi apute hwaohwo vwehwe. Na ushe waho Uzabeth aihupapila umwana. Olume na itawa lyakwe wayihumweta Yohana.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Nawe wabha nolunzongwo na shangwe nabhantu abhinji bhayihusongwa apapwa hwakwe.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Kwasababu ayibha gosi hwitagalile gosi sagayimwela idivai wala akholwe wape aimemezewe.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Upepo umwololo hata afume mvyanda mwanyi wakwa Na abhini abha Israeli aibhaweziye hwa gosi UNGOLOBHE wao.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Wapa aitangulila hwitalilo lyakwe ne roho ye hwa Eliya. Enguvu zwakwe ili agagalusye amoyo gabhuise igabhalile abhana, na abhabheshela bhabhatejile enjele ezye bhelyoli na hubheshele ugosi tayali abhantu bhabhalenganyinziwe.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zakaria abholele malaika, “Naimayawele izu ulyo eshi endigogolo na ushe wane gogolo wensiku nyinji.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Umalaika wagalula wabhozya, “Ane ne Gabrieli, nenemeleye, hwitagalalilo lya NGOLOBHE. Nane entunuwilye anjanje nawe, na hubhole lenongwa ezi enyinza.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Na nyenye, ubhabhe bubu, sobhayanje, mpaka isiku lila nayayibhombeha. Ego kwasababu sewahovwezye enongwa zyane gape gayitimila huwakati wakwe.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Nabhala abhantu bhalibhahugolela uZakaria. Bhaswiga akhalilihwakwe mla mshibhanza.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Nawafuma alisagawezya, ayanje nao bhamenye aje. alolile amaono mhati mshibhanza. Wape ahendeleye abhalolesya akhale abhebubu.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Zyabha ensiku ezye utumishi wakwe nuzyafiha abhalile akhaya yakwe.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Huta ensiku zila ushe wakwe ulizabethi apate evyanda wabha na amezi gasanu. Nawayanga, “
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Eshi shambombeye UGOSI ensiku zila zyanenyizya esoni yane hwitagalilo elyabhantu.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Umwezi uwa tanda umalaika uGabrieli asontezywe no NGOLOBHE abhalile mpaka mji wa hu Galilaya, itawa lyakwe Nazareti,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 Hwa rendu ubikira ya pabhiliwa no muntu itawa lyakwe Yusufu. Wa hutali hwa Daudi, na itawa lyakwe ubikira uyo yu Mariamu.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Ahinjila munyumba yakwe wayanga, “Mwagona, upewewe eneema! no GOSI alipandwemo nawe.”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Wapa ashelile tee afwatana nenongwazyakwe. Asebha humwoyo endamuho ene yeshe.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Umalaika abhola, “Ugaje hogope, Mariamu, afwanaje upate eneema afume hwa NGOLOBHE.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Enya ubhahweje, uyanda na pape umewna ulume, na itawa lyakwe ubha hwumwete u 'Yesu.'
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Oyo aibha GOSI abhahwetwe mwana yali humwanya uGOSI UNGOLOBHE alihupela itengo elye umwene u Daudi use wakwe.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 Abhaitawale ekhaya eya Yakobo wilawila na umwene wakwe sewayibha no umalisholo. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 UMariamu wabhola umalaika, zibhabhe wele enongwa ezi, afwanaje semenye ulume?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 UMalaika wajibu wabhola, “Upepo Uselu abhahumwenzele pamwanya yaho, na engulu zyakwe yalipamwanya zibhahu vwenwsye. Neshe izyongozi afwatanaje oyo yayipapwa ayibha zelu mwana wa NGOLOBHE.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Antele, enye uholo waho Elizabeti wape apete ulyanda ulya mwana ulume.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Afwatanaje nalimo izu lyasagaliwezehala hwa NGOLOBHE.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 UMariamu wayanga, “Waga, enye ane endi wembombo wa GOSI. Ebhehuline neshe shoyajele.” Antele umalaika wasogola wabhala hwamwahale.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Basi u Mariamu wasogola ensiku ezyo wabhola hata ensi ya humagamba nanali mpaka ensi emo ya hwa Yudea.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Winjelo munyumba mwa Zekaria walamuha u Elizabeti.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Yabha, Elizabeti nahwovwa hula alamushe kwakwe uMariamu, ahana ahela handa ahwanje mvyanda vyakwe, Elizabeti wamema opepo Uzelu.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Wakhola hwizu elyemaha wanyaga usayilye, “Hwabhashe bhonti nawe empapwo yaho esaiwe.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Unfumiye izu eli, hata omaye uwu GOSI wane anenzelene?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Nenshe izu ilyalamusha gane ahana ahela hanga hasongwelwe mhati mvyanda vyane.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Wape nafu yayovyezye neshe naga itimila gabholelwe no GOSI.”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Omariamu wayanga, omwoyo gwane gwamwenye ONGOLOBHE,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Roho yane esongwezye ONGOLOBHE yanauye ane.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Afwanaje agwenyizye unyonge uwe mbombo wakwe. Eshe, enyaga ahwandileshi evikholo vyonti vyayikwizya osayilwe.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Afwatanaje owemaha ambombeye amagasi, lyape itawalyakwa lizelu.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 ERehema zyakwe zidela evikholo ne vikholo hwebho bhahahuputa.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Abhombile amaha uhukhono gwakwe; abhanyampenye abhemashento afume masebho ezye moyo gabho.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Abhagwisizye agosi mmatengo gabho ageshimwene na nyonge abhabhosezye.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Abhenzala abhakutizizye aminza, bhape abhemali abhefwizye makhono wene.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Amwavwizye u Israeli uwembombo wakwa ili ahwizushe rehema zyakwe.
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 (Neshe shubhabhozezye ababa bhetu) Ibrahimu empapwo yakwe mpaka welawila.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 UMariamu wakhala nawo mpaka amezi gatatu nantele wawela abheale akhayayakwe.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Zyabha ensiku ezya pape hwakwe u Elizabeti nazya timila, wapapa umwana lume.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Bhahovwezye ajirani na mwabho bhakwe, aje GOSI amwonjezyezye erehema bhasongwa pandwemo nao.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Lyabha isiku elya nane wakati wa kutahiri omwana. Bhahanza hupele itawa elyayise, “Zakaria,”
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Unyino wakwe wagalula wayanga, “Nkashele; seshasho basi ayibha yo Yohana.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Bhabhola sepali amuntu afume hwamwenyu bhaho akwiziwe itawa elya Yohana.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Bhamwanya usewakwe sabhu hwmwete.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Wanza ahabampa wasimba aje, “itawa lyakwe yo Yohana.” Bhaswijitie bhonti.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Pepo na pepo ilomu lyakwe liguha numele lyakwe antele wanda ayaje. Nautelele ONGOLOBHE.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Bhinjilwa nowoga bhonti bhali bhakheye pandwemo, na. mambo ego gonti gatangazezwe ensi yonti yammagamba mgamba e Yudea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Na bhonti bhabhagovwezye bhagabheha humoyo gabho, bhayanga, “Umwana uno ayibha wefwane hwele?” Afwaneje ukhono ogwa GOSI gwali pandwemo no mwane.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 UZakaria uyise wamema opepo ozelu, wakuwawanyanga,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Abhosewe OGSI, ONGOLOBHE wa Israeli, afwanaje abhenzeye abhantu bhakwe na bhaule.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Atemelesezye empeta eyataule afume mlyango ugwa Daudi, uwe mbombo wakwe.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 Nenshe ayanjile afume huwandilo hwilumu elyakuwe akuwe bhakwe azelu. (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Tisatulwe na bhibhi bhentu na mma khono gabho bhonti bhabhativitwa
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Ili abhabhombele aminza ababa bhetu na hwizushe ipatano lyakwe izelu,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Ishilapo shalapiye Ibrahimu uyise wetu.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Afwanaje anzatavwilizya ate taushe nimakhono gabhibhi bhetu na humpute bila woga.
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 Nazelu nelyoli hwitagalilo lyakwe ensiku zyonti.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Nawe, womwana wahwetwa, ukuwe ukuwe wakwe yalimwanya, afwaneje awa wayitangulila hwita galila humaso ega GOSI ulenga nyizizye amadala gakwe,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Obhabhozye abhantu bhakwa usatule aje asajilwe embibhi zyabho.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Hwidala elye rehema lya NGOLOBHE wetu, afwatanaje hwezyo okhozyo lwalufumile amwanya lutifishiye,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Abhakhozye bhabhakhala hukisi hunzunda eyenfwa. nagalongozwa unamana getu hwidala ilinza.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Ula, mwana wakula wonjelela amaha roho wakhala humapoli hata hwisiku elye fumila hwakwe u Israeli.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luka 1 >