< Lucas 1 >

1 Since muitos se comprometeram a colocar em ordem uma narrativa a respeito daqueles assuntos que foram cumpridos entre nós,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 mesmo quando aqueles que desde o início foram testemunhas oculares e servidores da palavra nos entregaram,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it também me pareceu bom, tendo traçado o curso de todas as coisas com precisão desde o primeiro, para escrever a você em ordem, o mais excelente Teófilo;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 para que você possa saber a certeza a respeito das coisas em que você foi instruído.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Havia nos dias de Herodes, o rei da Judéia, um certo sacerdote chamado Zacarias, da divisão sacerdotal de Abijah. Ele tinha uma esposa das filhas de Aarão, e seu nome era Isabel.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ambos eram justos diante de Deus, andando sem culpa em todos os mandamentos e ordenanças do Senhor.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Mas elas não tinham filhos, porque Isabel era estéril, e ambas estavam bem avançadas em anos.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Agora, enquanto ele executava o ofício sacerdotal diante de Deus na ordem de sua divisão
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 de acordo com o costume do ofício sacerdotal, sua sorte era entrar no templo do Senhor e queimar incenso.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Toda a multidão do povo estava orando do lado de fora na hora do incenso.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Apareceu-lhe um anjo do Senhor, de pé no lado direito do altar do incenso.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zacarias ficou perturbado quando o viu, e o medo caiu sobre ele.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Mas o anjo lhe disse: “Não tenha medo, Zacarias, porque seu pedido foi ouvido. Sua esposa, Elizabeth, lhe dará um filho, e você chamará seu nome de João.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Você terá alegria e alegria, e muitos se regozijarão com seu nascimento.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Pois ele será grande aos olhos do Senhor, e não beberá vinho nem bebida forte. Ele será cheio do Espírito Santo, mesmo desde o ventre de sua mãe.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Ele voltará muitos dos filhos de Israel para o Senhor seu Deus.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Ele irá diante dele no espírito e no poder de Elias, 'para converter os corações dos pais aos filhos' e dos desobedientes à sabedoria dos justos; para preparar um povo preparado para o Senhor”.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zacharias disse ao anjo: “Como posso ter certeza disso? Pois eu sou um homem velho, e minha esposa está bem avançada em anos”.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 O anjo lhe respondeu: “Eu sou Gabriel, que estou na presença de Deus. Fui enviado para falar com vocês e trazer-lhes esta boa notícia”.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Eis que você ficará em silêncio e não poderá falar até o dia em que estas coisas acontecerão, porque não acreditou nas minhas palavras, que serão cumpridas no seu devido tempo”.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 O povo estava esperando por Zacarias, e eles se maravilharam com o fato de ele se ter atrasado no templo.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Quando ele saiu, ele não podia falar com eles. Eles perceberam que ele tinha visto uma visão no templo. Ele continuou fazendo sinais para eles, e permaneceu mudo.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Quando os dias de seu serviço foram cumpridos, ele partiu para sua casa.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Depois desses dias Elizabeth sua esposa concebeu, e ela se escondeu cinco meses, dizendo:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “Assim me fez o Senhor nos dias em que olhou para mim, para tirar minha reprovação entre os homens”.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Agora, no sexto mês, o anjo Gabriel foi enviado de Deus para uma cidade da Galiléia chamada Nazaré,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 para uma virgem prometida em casamento com um homem cujo nome era José, da casa de Davi. O nome da virgem era Maria.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Having entre, o anjo lhe disse: “Alegre-se, você a favoreceu muito! O Senhor está com você. Abençoada sejais vós entre as mulheres”.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Mas quando ela o viu, ficou muito perturbada com o ditado, e considerou que tipo de saudação isso poderia ser.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 O anjo lhe disse: “Não tenha medo, Maria, pois você encontrou favor com Deus.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Eis que conceberás em teu ventre e darás à luz um filho, e lhe darás o nome de “Jesus”.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Ele será grande e será chamado o Filho do Altíssimo. O Senhor Deus lhe dará o trono de seu pai David,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 e ele reinará sobre a casa de Jacó para sempre. Não haverá fim para o seu Reino”. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Mary disse ao anjo: “Como isso pode ser, vendo que sou virgem”?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 O anjo lhe respondeu: “O Espírito Santo virá sobre você, e o poder do Altíssimo o ofuscará”. Portanto, também o santo que nascer de vós será chamado Filho de Deus.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Eis que Isabel, sua parente, também concebeu um filho em sua velhice; e este é o sexto mês com ela que foi chamada estéril.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Pois nada do que Deus diz é impossível”.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Maria disse: “Eis o servo do Senhor; faça-se em mim segundo a vossa palavra”. Então o anjo se afastou dela.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Maria levantou-se naqueles dias e entrou apressadamente no país das colinas, em uma cidade de Judá,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 e entrou na casa de Zacarias e cumprimentou Isabel.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Quando Elizabeth ouviu a saudação de Maria, o bebê saltou em seu ventre; e Elizabeth foi cheia do Espírito Santo.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Ela chamou em voz alta e disse: “Bendita és tu entre as mulheres, e bendito é o fruto do teu ventre!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Why sou tão favorecida, que a mãe de meu Senhor deveria vir a mim?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Pois eis que, quando a voz de vossa saudação chegou a meus ouvidos, o bebê saltou de alegria em meu ventre!
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Bem-aventurada aquela que acreditou, pois haverá um cumprimento das coisas que lhe foram ditas pelo Senhor”!
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Disse Mary, “Minha alma engrandece o Senhor”.
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Meu espírito rejubilou em Deus, meu Salvador,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 pois ele olhou para o humilde estado de seu servo. Pois eis que de agora em diante, todas as gerações me chamarão de abençoado.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Para aquele que é poderoso, fez grandes coisas por mim. Santo é seu nome.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Sua misericórdia é por gerações e gerações para com aqueles que o temem.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Ele mostrou força com seu braço. Ele espalhou o orgulho na imaginação de seus corações.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Ele derrubou príncipes de seus tronos, e tem exaltado os humildes.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Ele encheu os famintos de coisas boas. Ele mandou os ricos embora vazios.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Ele deu ajuda a Israel, seu servo, para que ele pudesse se lembrar da misericórdia,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 enquanto ele falava com nossos pais, a Abraão e sua descendência para sempre”. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Mary ficou com ela cerca de três meses, e depois voltou para sua casa.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Agora o tempo em que Elizabeth deveria dar à luz foi cumprido, e ela deu à luz a um filho.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Seus vizinhos e parentes ouviram que o Senhor tinha aumentado sua misericórdia para com ela, e se regozijaram com ela.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 No oitavo dia, eles vieram para circuncidar a criança; e o teriam chamado de Zacarias, depois do nome de seu pai.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Sua mãe respondeu: “Não é assim; mas ele será chamado João”.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Eles disseram a ela: “Não há ninguém entre seus parentes que seja chamado por este nome”.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Eles fizeram sinais para seu pai, como ele gostaria que ele o chamasse.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Ele pediu uma tábua de escrever, e escreveu: “Seu nome é John”. Todos eles se maravilharam.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Sua boca foi aberta imediatamente e sua língua libertada, e ele falou, abençoando a Deus.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 O medo veio sobre todos os que viviam ao seu redor, e todos estes ditados foram falados em toda a região montanhosa da Judéia.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Todos os que os ouviram os deitaram em seu coração, dizendo: “O que será então esta criança”? A mão do Senhor estava com ele.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Seu pai Zacharias foi cheio do Espírito Santo, e profetizou, dizendo,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Bendito seja o Senhor, o Deus de Israel”, pois ele visitou e resgatou seu povo;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 e levantou um chifre de salvação para nós na casa de seu servo David
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (como ele falou pela boca de seus santos profetas que foram de outrora), (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvação de nossos inimigos e da mão de todos os que nos odeiam;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 para mostrar misericórdia para com nossos pais, para lembrar seu santo pacto,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 o juramento que ele fez a Abraão, nosso pai,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 para nos conceder que nós, sendo libertados das mãos de nossos inimigos, deve servi-lo sem medo,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 em santidade e retidão diante dele todos os dias de nossa vida.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 E você, criança, será chamada de profeta do Altíssimo; pois você irá diante da face do Senhor para preparar seus caminhos,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 para dar conhecimento da salvação a seu povo através da remissão de seus pecados,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 por causa da terna misericórdia de nosso Deus, pelo qual o amanhecer do alto nos visitará,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 para brilhar sobre aqueles que se sentam na escuridão e na sombra da morte; para guiar nossos pés para o caminho da paz”.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 A criança estava crescendo e se tornando forte em espírito, e esteve no deserto até o dia de sua aparição pública em Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Lucas 1 >