< Lucas 1 >

1 Como você sabe, muitas pessoas têm se esforçado para escrever as coisas que têm acontecido relacionadas a nós.
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Elas se basearam em evidências transmitidas por testemunhas e por ministros da Palavra, que acompanharam esses fatos desde o início.
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Então, eu também decidi que, por ter investigado com muito cuidado o que ocorreu desde o início, seria uma boa ideia escrever um relato preciso de tudo o que aconteceu.
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Eu fiz isso, querido Teófilo, para que você tenha certeza de que aquilo que lhe foi ensinado é totalmente verdadeiro.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Durante o tempo em que Herodes governou a Judeia, havia um sacerdote chamado Zacarias, que era do grupo dos sacerdotes de Abias. Ele se casou com Isabel, que era descendente de Arão, o sacerdote.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ambos viviam de maneira justa diante de Deus, sendo muito cuidadosos em seguir todos os mandamentos e todas as leis do Senhor.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Eles não tinham filhos, porque Isabel não podia ter filhos, e os dois já eram muito idosos.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Enquanto Zacarias estava fazendo o seu trabalho como sacerdote diante de Deus, representando seu grupo de sacerdotes,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 ele foi escolhido entre vários, de acordo com o costume da época, para entrar no Templo do Senhor e queimar o incenso.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Durante o tempo da oferta de incenso, uma grande multidão estava orando do lado de fora do Templo.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Um anjo do Senhor apareceu para Zacarias, ficando à direita do altar de incenso.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Quando Zacarias viu o anjo, ele ficou espantado e com muito medo.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Mas, o anjo lhe disse: “Não tenha medo, Zacarias! A sua oração foi ouvida. Isabel, sua esposa, lhe dará um filho e vocês devem chamá-lo João.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Ele lhe trará muita alegria e felicidade e muitas pessoas festejarão o seu nascimento.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Ele será importante aos olhos do Senhor. Ele não deverá beber vinho ou qualquer outra bebida alcoólica. Ele será cheio do Espírito Santo, mesmo antes do seu nascimento.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Ele fará com que muitos israelitas se voltem para o Senhor, o seu Deus.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Ele preparará o caminho para o Senhor com o mesmo ânimo e poder de Elias, para fazer com que os pais e seus filhos façam as pazes e para que os rebeldes voltem para o caminho certo e, assim, preparem o povo para o Senhor.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 “Como eu posso ter certeza disso?” Zacarias perguntou ao anjo. “Eu sou velho e minha esposa também está envelhecendo.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 O anjo respondeu: “Eu sou Gabriel. Sirvo a Deus e fui enviado para lhe dar essa boa notícia.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Mas, já que não acreditou no que eu lhe disse, você ficará mudo, incapaz de falar, até que minhas palavras se cumpram”.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Do lado de fora do Templo, as pessoas esperavam que Zacarias saísse, pensando no motivo dele estar demorando tanto lá dentro.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Quando finalmente ele saiu, não conseguia falar com eles. Eles perceberam que ele tinha tido uma visão no Templo, pois embora pudesse gesticular e se expressar, estava completamente mudo.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Após haver terminado seus dias de serviço no Templo, ele voltou para casa.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Algum tempo depois, sua esposa, Isabel, engravidou. Ela ficou em casa, sem sair, durante cinco meses.
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Isabel disse: “O Senhor fez isso por mim. Agora, a vergonha que eu sentia diante dos outros acabou!”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 No sexto mês de sua gravidez, Deus enviou o anjo Gabriel para uma jovem chamada Maria, que vivia na cidade de Nazaré, na Galileia.
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 Ela estava noiva de um homem chamado José.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 O anjo a cumprimentou. Ele lhe disse: “Você é muito abençoada! O Senhor está com você!”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Maria estava muito confusa com o que ele disse e imaginava qual seria o significado desse cumprimento.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 O anjo continuou: “Não se preocupe, Maria, pois Deus veio demonstrar sua bondade para você!
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Você ficará grávida e dará à luz um filho. Você deverá chamá-lo Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Ele será muito importante e será conhecido como o Filho do Altíssimo. Deus, o Senhor, dará para ele o trono de Davi, seu pai,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 e ele reinará sobre a casa de Jacó para sempre. Seu Reino nunca se acabará.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Maria perguntou: “Como isso é possível? Eu ainda sou virgem!”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Ele respondeu: “O Espírito Santo virá sobre você e o poder do Altíssimo a envolverá. O bebê que nascerá será santo e será chamado de Filho de Deus.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 E até Isabel, a sua parenta, está grávida mesmo sendo mais velha. A mulher que todos diziam que não podia ter filhos já está no sexto mês de gravidez.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Nada é impossível para Deus.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Maria disse: “Aqui estou eu, pronta para ser a serva de Deus! Que aconteça comigo exatamente como você disse!” Então, o anjo foi embora.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Pouco tempo depois, Maria se preparou e foi depressa para as colinas da Judeia, para a cidade em que
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Zacarias e sua mulher moravam. Ela chamou Isabel assim que chegou.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 No mesmo instante em que Isabel ouviu a voz de Maria, o bebê sentiu tanta alegria que mexeu dentro da sua barriga. Então, tomada pelo poder do Espírito Santo, Isabel
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 falou bem alto: “Você é a mais abençoada das mulheres, e a criança que nascerá de você também será abençoada!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Quem sou eu para receber a visita da mãe do meu Senhor?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Assim que ouvi você me cumprimentar, o meu bebê se mexeu dentro da minha barriga, de tanta alegria que sentiu.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Como você é abençoada! Pois você acredita que o Senhor fará o que lhe prometeu!”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Maria respondeu: “Eu louvo ao Senhor!
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Estou tão feliz com Deus, meu Salvador!
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Pois ele decidiu que eu, sua serva, era digna de sua consideração, apesar de minha origem humilde. De agora em diante, todos dirão que eu fui abençoada,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 pois o Deus Poderoso fez coisas maravilhosas por mim. Seu nome é santo.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 A sua bondade passa de geração em geração para aqueles que o respeitam.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Com o seu poder, ele destrói os que, com arrogância, pensam que são muito espertos.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Ele tira de seus tronos reis poderosos e põe em altas posições os humildes.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Ele dá aos que têm fome boas coisas para comer e manda os ricos embora de mãos vazias.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Exatamente como prometeu aos nossos antepassados, ele ajudou o povo de Israel, seu servo.
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 E se lembrou de demonstrar piedade para Abraão e seus descendentes para sempre.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Maria ficou com Isabel por três meses e, depois, voltou para sua casa.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Chegou o momento de Isabel ter seu bebê, e ela deu à luz um menino.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Seus vizinhos e parentes ouviram falar de como o Senhor tinha demonstrado sua imensa bondade com Isabel e foram comemorar junto com ela.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Oito dias depois, vieram para fazer a circuncisão do menino. E eles queriam chamar o bebê de Zacarias, em homenagem a seu pai.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Mas, Isabel disse: “Não! Ele deve se chamar João.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Eles lhe disseram: “Mas, nenhum dos nossos parentes tem esse nome.”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Gesticulando, eles perguntaram ao pai da criança, Zacarias, qual nome ele queria para o seu filho.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Zacarias mostrou, por meio de gestos, que queria algo em que pudesse escrever. Para a surpresa de todos, ele escreveu: “Seu nome é João.”
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Imediatamente, ele voltou a falar e começou a louvar a Deus.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Todos os vizinhos ficaram assombrados com o que havia acontecido, e a notícia se espalhou por toda a região montanhosa da Judeia.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Todos os que ouviam a notícia pensavam sobre o significado dela. Eles perguntavam: “O que o pequenino vai ser quando crescer?” Pois era certo que o menino era muito especial para Deus.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Zacarias, seu pai, cheio do Espírito Santo, fez esta profecia:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “O Senhor, o Deus de Israel, é maravilhoso, pois ele veio para o seu povo e o libertou.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Ele nos deu um grande Salvador, descendente do seu servo Davi,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 exatamente como tinha prometido, por intermédio dos seus santos profetas, muito tempo atrás. (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Ele prometeu nos salvar dos nossos inimigos, daqueles que nos odeiam.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Ele foi bondoso para os nossos ancestrais, lembrando-se da sua santa aliança.
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Ele fez uma promessa para o nosso antepassado Abraão.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Ele nos libertou do medo e nos resgatou das mãos dos nossos inimigos,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 para que possamos servi-lo, fazendo o que é bom e certo por toda a nossa vida.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Apesar de você ser apenas uma criancinha, será chamado profeta do Altíssimo, pois você irá à frente do Senhor, para lhe preparar o caminho.
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Você anunciará a salvação ao povo de Deus, que virá por meio do perdão dos pecados deles.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Pela bondade e cuidado do nosso Deus, o sol nascente, vindo do céu, irá descer sobre nós,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 para iluminar aqueles que vivem nas trevas e na sombra da morte e para nos guiar pelo caminho da paz.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 O menino João cresceu e se tornou espiritualmente forte. Ele viveu no deserto, até que chegou o momento de se apresentar ao povo de Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Lucas 1 >