< Lucas 21 >

1 E ele, olhando, viu os ricos lançarem suas ofertas na arca do tesouro [do templo].
Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
2 E viu também uma pobre viúva lançar ali duas pequenas moedas.
Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
3 E disse: Em verdade vos digo que esta pobre viúva lançou mais do que todos,
Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
4 Porque todos aqueles lançaram para as ofertas de Deus daquilo que lhes sobrava; mas esta [viúva], de sua pobreza, lançou todo o sustento que tinha.
Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
5 E alguns estavam falando do templo, que era adornado com formosas pedras e ofertas. Então [Jesus] disse:
Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
6 Destas coisas que vedes, dias virão, em que não se deixará pedra sobre pedra, que não seja derrubada.
“Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
7 E perguntaram-lhe, dizendo: Mestre, quando, pois, serão essas coisas? E que sinal haverá, quando essas coisas vierem a acontecer?
Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
8 Então ele disse: Olhai para que não vos enganem, porque muitos virão em meu nome, dizendo: Eu sou [o Cristo]. E o tempo já está perto; portanto não os sigais.
Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
9 E quando ouvirdes de guerras, e de rebeliões, não vos espanteis. Porque é necessário que estas coisas aconteçam primeiro; mas ainda não é o fim.
Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
10 Então lhe disse: Então se levantará nação contra nação, e reino contra reino.
Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
11 E haverá em vários lugares grandes terremotos e fomes, e pragas; haverá também coisas espantosas, e grandes sinais do céu.
Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
12 Mas antes de tudo isto, eles vos impedirão e vos perseguirão, [vos] entregando em sinagogas e prisões, [e] vos trazendo diante de reis, e governadores, por causa do meu nome.
“Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
13 E isto vos acontecerá para haver testemunho.
Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
14 Portanto, que vós decidais nos vossos corações não planejar como direis em vossa defesa,
Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
15 porque eu vos darei boca e sabedoria, para que todos os que forem contra vós não posam [vos] contradizer ou resistir.
Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
16 E vós sereis entregues até pelos pais, e irmãos, e parentes, e amigos; e [alguns] de vós serão mortos.
Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
17 E vós sereis odiados por todos por causa do meu nome.
Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
18 Mas nem um cabelo de vossa cabeça parecerá.
Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
19 Por vossa paciência ganhareis vossas almas.
Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
20 Porém quando virdes a Jerusalém cercada de exércitos, sabei então, que próxima está sua desolação.
“In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
21 Então, os que estiverem na Judeia, fujam para os montes; e os que estiverem no meio dela, saiam, e os que estiverem nos campos, não entrem nela.
A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
22 Porque estes são dias de vingança, para que todas as coisas que estão escritas se cumpram.
Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
23 Mas ai das grávidas, e das que amamentarem naqueles dias; porque grande calamidade haverá na terra, e ira contra este povo.
Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
24 E cairão pela lâmina de espada, e serão levados cativos para todas as nações; e Jerusalém será pisada pelos gentios, até que os tempos dos gentios se cumpram.
Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
25 E haverá sinais no Sol, [na] Lua, e [nas] estrelas; e na terra sofrimento entre as nações, como o rugir e agitar do mar.
“Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
26 As pessoas desmaiarão de medo e da expectativa das coisas que vão acontecer ao mundo, porque os poderes dos céus serão abalados.
Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
27 E então verão o Filho do homem vir em uma nuvem com grande poder e glória.
A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
28 Ora, quando estas coisas começarem a acontecer, olhai para cima, e levantai vossas cabeças, porque vosso resgate está perto.
Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
29 E disse-lhes uma parábola: Olhai a figueira, e todas as árvores;
Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
30 Quando vós vedes elas já brotando, sabeis por vós mesmos que o verão já está perto.
A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
31 Assim também vós, quando virdes acontecer estas coisas, sabei que o Reino de Deus já está perto.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
32 Em verdade vos digo, que esta geração não passará, até que tudo aconteça.
“Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
33 O céu e a terra passarão, mas minhas palavras de maneira nenhuma passarão.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
34 E olhai por vós, para que vossos corações não venham a se encher de ressaca e embriaguez, e das preocupações d [esta] vida; e vos venha aquele dia de surpresa.
“Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
35 Porque virá como uma armadilha sobre todos os que habitam sobre a face de toda a terra.
Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
36 Então vigiai sempre, orando para que sejais considerados dignos de escaparem de todas as coisas que irão acontecer, e de ficarem de pé diante do Filho do homem.
Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
37 E ensinava durante os dias no Templo, porém, às noites saía e as passava no monte, chamado as Oliveiras.
Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
38 E todo o povo vinha até ele de manhã cedo ao templo, para o ouvir.
Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.

< Lucas 21 >