< Lamentações de Jeremias 5 >

1 Lembra-te, SENHOR, do que tem nos acontecido; presta atenção e olha nossa humilhação.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Nossa herança passou a ser de estrangeiros, nossas casas de forasteiros.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 Órfãos somos sem pai, nossas mães são como viúvas.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 Bebemos nossa água por dinheiro; nossa lenha temos que pagar.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Perseguição sofremos sobre nossos pescoços; estamos cansados, mas não temos descanso.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 Nós nos rendemos aos egípcios e aos assírios para nos saciarmos de pão.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Nossos pais pecaram, e não existem mais; porém nós levamos seus castigos.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Servos passaram a nos dominar; ninguém há que [nos] livre de suas mãos.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 Com risco de vida trazemos nosso pão, por causa da espada do deserto.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Nossa pele se tornou negra como um forno, por causa do ardor da fome.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Abusaram das mulheres em Sião, das virgens nas cidades de Judá.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Os príncipes foram enforcados por sua mãos; não respeitaram as faces dos velhos.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Levaram os rapazes para moer, e os moços caíram debaixo da lenha [que carregavam].
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 Os anciãos deixaram de [se sentarem] junto as portas, os rapazes de suas canções.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Acabou a alegria de nosso coração; nossa dança se tornou em luto.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 Caiu a coroa de nossa cabeça; ai agora de nós, porque pecamos.
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Por isso nosso coração ficou fraco, por isso nossos olhos escureceram;
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 Por causa do monte de Sião, que está desolado; raposas andam nele.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Tu, SENHOR, permanecerás para sempre; [e] teu trono de geração após geração.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Por que te esquecerias de nós para sempre e nos abandonarias por tanto tempo?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Converte-nos, SENHOR, a ti, e seremos convertidos; renova o nossos dias como antes;
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 A não ser que tenhas nos rejeitado totalmente, e estejas enfurecido contra nós ao extremo.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Lamentações de Jeremias 5 >