< 38 >

1 Então o SENHOR respondeu a Jó desde um redemoinho, e disse:
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Quem é esse que obscurece o conselho com palavras sem conhecimento?
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Agora cinge teus lombos como homem; e eu te perguntarei, e tu me explicarás.
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Onde estavas tu quando eu fundava a terra? Declara- [me], se tens inteligência.
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 Quem determinou suas medidas, se tu o sabes? Ou quem estendeu cordel sobre ela?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 Sobre o que estão fundadas suas bases? Ou quem pôs sua pedra angular,
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 Quando as estrelas do amanhecer cantavam alegremente juntas, e todos os filhos de Deus jubilavam?
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 Ou [quem] encerrou o mar com portas, quando transbordou, saindo da madre,
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 Quando eu pus nuvens por sua vestidura, e a escuridão por sua faixa;
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 Quando eu passei sobre ele meu decreto, e [lhe] pus portas e ferrolhos,
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 E disse: Até aqui virás, e não passarás adiante, e aqui será o limite para a soberba de tuas ondas?
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 Desde os teus dias tens dado ordem à madrugada? [Ou] mostraste tu ao amanhecer o seu lugar,
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 Para que tomasse os confins da terra, e os perversos fossem sacudidos dela?
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 E [a terra] se transforma como barro [sob] o selo; [todas as coisas sobre ela] se apresentam como vestidos?
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 E dos perversos é desviada sua luz, e o braço erguido é quebrado.
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Por acaso chegaste tu às fontes do mar, ou passeaste no mais profundo abismo?
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Foram reveladas a ti as portas da morte, ou viste as portas da sombra de morte?
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 Entendeste tu as larguras da terra? Declara, se sabes tudo isto.
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 Onde está o caminho [por onde] mora a luz? E quanto às trevas, onde fica o seu lugar?
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 Para que as tragas a seus limites, e conheças os caminhos de sua casa.
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Certamente tu o sabes, pois já eras nascido, e teus dias são inúmeros!
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 Por acaso entraste tu aos depósitos da neve, e viste os depósitos do granizo,
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 Que eu retenho até o tempo da angústia, até o dia da batalha e da guerra?
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 Onde está o caminho em que a luz se reparte, e o vento oriental se dispersa sobre a terra?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Quem repartiu um canal às correntezas de águas, e caminho aos relâmpagos dos trovões,
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 Para chover sobre a terra [onde] havia ninguém, [sobre] o deserto, onde não há gente,
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 Para fartar [a terra] deserta e desolada, e para fazer crescer aos renovos da erva.
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 Por acaso a chuva tem pai? Ou quem gera as gotas do orvalho?
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 De qual ventre procede o gelo? E quem gera a geada do céu?
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 As águas se tornam duras como pedra, e a superfície do abismo se congela.
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Podes tu atar as cadeias das Plêiades, ou desatar as cordas do Órion?
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Podes tu trazer as constelações a seu tempo, e guiar a Ursa com seus filhos?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Sabes tu as ordenanças dos céus? Ou podes tu dispor do domínio deles sobre a terra?
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Ou podes levantar tua voz até às nuvens, para que a abundância das águas te cubra?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Podes tu mandar relâmpagos, para que saiam, e te digam: Eis-nos aqui?
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Quem pôs a sabedoria no íntimo? Ou quem deu entendimento à mente?
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Quem pode enumerar as nuvens com sabedoria? E os odres dos céus, quem pode os despejar?
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 Quando o pó se endurece, e os torrões se apegam uns aos outros?
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 Caçarás tu a presa para o leão? Ou saciarás a fome dos leões jovens,
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 Quando estão agachados nas covas, [ou] estão à espreita no matagal?
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 Quem prepara aos corvos seu alimento, quando seus filhotes clamam a Deus, andando de um lado para o outro por não terem o que comer?
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?

< 38 >