< Lucas 21 >

1 E, olhando ele, viu os ricos lançarem as suas ofertas na arca do tesouro;
Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
2 E viu também uma pobre viúva lançar ali duas pequenas moedas;
Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
3 E disse: Em verdade vos digo que lançou mais do que todos esta pobre viúva;
Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
4 Porque todos aqueles deitaram para as ofertas de Deus, do que lhes sobeja; mas esta, da sua pobreza, deitou todo o sustento que tinha.
Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
5 E, dizendo alguns a respeito do templo, que estava ornado de formosas pedras e dádivas, disse:
Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
6 Quanto a estas coisas que vêdes, dias virão em que se não deixará pedra sobre pedra, que não seja derribada.
“Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
7 E perguntaram-lhe, dizendo: Mestre, quando serão pois estas coisas? E que sinal haverá quando estas coisas estiverem para acontecer?
Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
8 Disse então ele: vede não vos enganem, porque virão muitos em meu nome, dizendo: Eu sou o Cristo, e já o tempo está próximo; não vades portanto após eles.
Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
9 E, quando ouvirdes de guerras e sedições, não vos assusteis. Porque é necessário que estas coisas aconteçam primeiro, mas o fim não será logo.
Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
10 Então lhes disse: levantar-se-a nação contra nação, e reino contra reino;
Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
11 E haverá em vários lugares grandes terremotos, e fomes e pestilências; haverá também coisas espantosas, e grandes sinais do céu.
Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
12 Mas antes de todas estas coisas lançarão mão de vós, e vos perseguirão, entregando-vos às sinagogas e às prisões, e conduzindo-vos à presença de reis e presidentes, por amor do meu nome.
“Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
13 E sobrevir-vos-a isto para testemunho.
Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
14 Proponde pois em vossos corações não premeditar como haveis de responder,
Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
15 Porque eu vos darei boca e sabedoria a que não poderão contradizer nem resistir todos quantos se vos opuserem.
Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
16 E até pelos pais, e irmãos, e parentes, e amigos sereis entregues; e matarão alguns de vós.
Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
17 E por todos sereis aborrecidos por amor do meu nome.
Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
18 Mas não perecerá nem um cabelo da vossa cabeça.
Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
19 Na vossa paciência possui as vossas almas.
Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
20 Porém, quando virdes Jerusalém cercada de exércitos, sabei então que já é chegada a sua assolação.
“In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
21 Então, os que estiverem na Judeia, fujam para os montes; e, os que estiverem no meio dela, saiam: e, os que nos campos, não entrem nela.
A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
22 Porque dias de vingança são estes, para que se cumpram todas as coisas que estão escritas.
Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
23 Mas ai das grávidas, e das que criarem naqueles dias! porque haverá grande aperto na terra, e ira sobre este povo.
Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
24 E cairão ao fio da espada, e para todas as nações serão levados cativos; e Jerusalém será pisada pelos gentios, até que os tempos dos gentios se completem.
Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
25 E haverá sinais no sol, e na lua e nas estrelas; e na terra aperto das nações em perplexidade, pelo bramido do mar e das ondas;
“Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
26 Homens desmaiando de terror, na expectação das coisas que sobrevirão ao mundo. Porque as virtudes do céu serão abaladas.
Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
27 E então verão vir o Filho do homem numa nuvem, com poder e grande glória.
A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
28 Ora, quando estas coisas começarem a acontecer, olhai para cima, e levantai as vossas cabeças, porque a vossa redenção está próxima.
Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
29 E disse-lhes uma parábola: olhai para a figueira, e para todas as árvores;
Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
30 Quando já tem brotado, vós sabeis por vós mesmos, vendo-as, que perto está já o verão.
A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
31 Assim também vós, quando virdes acontecer estas coisas, sabei que o reino de Deus está perto.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
32 Em verdade vos digo que não passará esta geração até que tudo aconteça.
“Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
33 Passará o céu e a terra, mas as minhas palavras não hão de passar.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
34 E olhai por vós, não aconteça que os vossos corações se carreguem de glutonaria, embriaguez, e dos cuidados desta vida, e venha sobre vós de improviso aquele dia.
“Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
35 Porque virá como um laço sobre todos os que habitam sobre a face de toda a terra.
Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
36 Vigiai pois em todo o tempo, orando, para que sejais havidos por dignos de evitar todas estas coisas que hão de acontecer, e de estar em pé diante do Filho do homem.
Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
37 E de dia ensinava no templo, e à noite, saindo, ficava no monte chamado das Oliveiras.
Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
38 E todo o povo ia ter com ele ao templo, de manhã cedo, para o ouvir.
Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.

< Lucas 21 >