< Lucas 17 >

1 E disse aos discípulos: É impossível que não venham escândalos, mas ai daquele por quem vierem!
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 Melhor lhe fôra que lhe pusessem ao pescoço uma mó de atafona, e fosse lançado ao mar, do que escandalizar um destes pequenos.
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 Olhai por vós mesmos. E, se teu irmão pecar contra ti, repreende-o, e, se ele se arrepender, perdoa-lhe.
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 E, se pecar contra ti sete vezes no dia, e sete vezes no dia tornar a ti, dizendo: Arrependo-me; perdoa-lhe.
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 Disseram então os apóstolos ao Senhor: acrescenta-nos a fé.
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 E disse o Senhor: Se tivesseis fé como um grão de mostarda, direis a esta amoreira: Desarreiga-te daqui, e planta-te no mar; e vos obedeceria.
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 E qual de vós terá um servo lavrando ou apascentando, e, voltando ele do campo, lhe diga: Chega-te, e assenta-te à mesa?
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 E não lhe diga antes: Prepara-me a ceia, e cinge-te, e serve-me, até que tenha comido e bebido, e depois comerás e beberás tu?
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 Porventura dá graças ao tal servo, porque fez o que lhe foi mandado? Creio que não.
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 Assim também vós, quando fizerdes tudo o que vos for mandado, dizei: Somos servos inúteis, porque fizemos somente o que devíamos fazer.
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 E aconteceu que, indo ele a Jerusalém, passou pelo meio da Samaria e da Galiléia;
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 E, entrando numa certa aldeia, sairam-lhe ao encontro dez homens leprosos, os quais pararam de longe;
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 E levantaram a voz, dizendo: Jesus, Mestre, tem misericórdia de nós.
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 E ele, vendo-os, disse-lhes: Ide, e mostrai-vos aos sacerdotes. E aconteceu que, indo eles, ficaram limpos.
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 E um deles, vendo que estava são, voltou glorificando a Deus em alta voz;
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 E caiu aos seus pés, com o rosto em terra, dando-lhe graças: e este era samaritano.
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 E, respondendo Jesus, disse: Não foram dez os limpos? E onde estão os nove?
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 Não houve quem voltasse a dar glória a Deus senão este estrangeiro?
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 E disse-lhe: Levanta-te, e vai; a tua fé te salvou.
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 E, interrogado pelos fariseus sobre quando havia de vir o reino de Deus, respondeu-lhes, e disse: O reino de Deus não vem com aparência exterior.
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 Nem dirão: ei-lo aqui, ou, ei-lo ali; porque eis que o reino de Deus está entre vós.
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 E disse aos discípulos: Dias virão em que desejareis ver um dos dias do Filho do homem, e não o vereis.
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 E dir-vos-ão: ei-lo aqui, ou, ei-lo ali está; não vades, nem os sigais:
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 Porque, como o relâmpago, fuzilando de uma parte debaixo do céu, resplandece até à outra debaixo do céu, assim será também o Filho do homem no seu dia.
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 Mas primeiro convém que ele padeça muito, e seja reprovado por esta geração.
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 E, como aconteceu nos dias de Noé, assim será também nos dias do Filho do homem:
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 Comiam, bebiam, casavam e davam-se em casamento, até ao dia em que Noé entrou na arca, e veio o dilúvio, e os consumiu a todos.
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 Como também da mesma maneira aconteceu nos dias de Lot: comiam, bebiam, compravam, vendiam, plantavam e edificavam.
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 Mas no dia em que Lot saiu de Sodoma, choveu do céu fogo e enxofre, e os consumiu a todos.
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 Assim será no dia em que o Filho do homem se há de manifestar.
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 Naquele dia, quem estiver no telhado, e as suas alfaias em casa, não desça a toma-las; e, da mesma sorte, o que estiver no campo não volte para traz.
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 Lembrai-vos da mulher de Lot.
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 Qualquer que procurar salvar a sua vida perde-la-á, e qualquer que a perder salva-la-a.
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 Digo-vos que naquela noite estarão dois numa cama; um será tomado, e outro será deixado.
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 Duas estarão juntas, moendo; uma será tomada, e outra será deixada.
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
36 Dois estarão no campo; um será tomado, o outro será deixado.
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 E, respondendo, disseram-lhe: Onde, Senhor? E ele lhes disse: Onde estiver o corpo, ai se ajuntarão as águias.
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”

< Lucas 17 >