< 2 João 1 >

1 O ancião à senhora eleita, e a seus filhos, aos quais amo na verdade, e não somente eu, mas também todos os que tem conhecido a verdade,
Dattijon nan, Zuwa ga uwargida zaɓaɓɓiya da kuma’ya’yanta, waɗanda nake ƙauna ƙwarai da gaske kuma ba ni kaɗai ba, amma har da dukan waɗanda suka san gaskiya.
2 Por amor da verdade que está em nós e para sempre estará conosco: (aiōn g165)
Muna ƙaunarku saboda gaskiyan nan, wadda take cikinmu za tă kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn g165)
3 Graça, misericórdia, paz, da parte de Deus Pai e da do Senhor Jesus Cristo, o Filho do Pai, seja convosco na verdade e caridade.
Alheri, jinƙai da kuma salama daga Allah Uba da kuma Yesu Kiristi, Ɗan Uba, su kasance tare da mu cikin gaskiya da ƙauna.
4 Muito me alegrarei por achar que alguns de teus filhos andam na verdade, assim como recebemos o mandamento do Pai.
Na yi farin ciki ƙwarai, da na sami waɗansu’ya’yanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda Uba ya umarce mu.
5 E agora, senhora, rogo-te, não como escrevendo-te um novo mandamento, mas aquele que desde o princípio tivemos, que nos amemos uns aos outros.
Yanzu kuma, uwargida ƙaunatacciya, ba sabon umarni nake rubuta miki ba sai dai wanda muke da shi tun farko. Ina roƙo cewa mu ƙaunaci juna.
6 E a caridade é esta: que andemos segundo os seus mandamentos. Este é o mandamento, como já desde o princípio ouvistes, que nele andeis.
Ƙauna, ita ce mu yi biyayya ga umarnansa. Kamar yadda kuka ji tun da fari, umarninsa shi ne ku yi zaman ƙauna.
7 Porque já muitos enganadores entraram no mundo, os quais não confessam que Jesus Cristo veio em carne. Este tal é o enganador e o anti-cristo.
Masu ruɗi da yawa, waɗanda ba su yarda da zuwan Yesu Kiristi cikin jiki ba, sun riga sun fito a duniya. Duk irin mutumin nan mai ruɗi ne kuma magabcin Kiristi.
8 Olhai por vós mesmos, para que não percamos o que já trabalhamos, antes recebamos o inteiro galardão.
Ku lura don kada ku yi hasarar aikin da kuka yi, sai dai ku sami cikakken lada.
9 Todo aquele que prevarica, e não persevera na doutrina de Cristo, não tem a Deus: quem persevera na doutrina de Cristo, esse tem assim ao Pai como ao Filho.
Duk mutumin da bai tsaya a kan koyarwar Kiristi ba, amma ya yi ƙari a kanta, mutumin nan ba shi da Allah. Amma wanda ya tsaya a kan koyarwar Kiristi, yana da Uban da kuma Ɗan.
10 Se alguém vem ter convosco, e não traz esta doutrina, não o recebais em casa, nem tampouco o saudeis.
Duk wanda ya zo wurinku bai kuma kawo koyarwan nan ba, kada ku karɓe shi a gidanku ko ku marabce shi.
11 Porque quem o saúda tem parte nas suas más obras.
Duk wanda ya karɓe shi yana tarayya da mugun aikinsa ke nan.
12 Muitas coisas tenho que escrever-vos, porém não quis com papel e tinta; mas espero ir ter convosco e falar de boca a boca, para que o nosso gozo seja cumprido.
Ina da abubuwa da dama da zan rubuta muku, sai dai ba na so in yi amfani da takarda da inki in rubuta. A maimako, ina fata in ziyarce ku in kuma yi magana da ku fuska da fuska, domin farin cikinmu yă zama cikakke.
13 Saúdam-te os filhos de tua irmã, a eleita. amém.
’Ya’yan’yar’uwarki wadda Allah ya keɓe, suna gaishe ku.

< 2 João 1 >