< Salmos 21 >

1 O rei se alegra em tua força, Senhor; e na tua salvação grandemente se regozija.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
2 Cumpriste-lhe o desejo do seu coração, e não negaste as supplicas dos seus labios (Selah)
Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
3 Pois o prevines das bençãos de bondade; pões na sua cabeça uma corôa d'oiro fino
Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
4 Vida te pediu, e lh'a déste, mesmo longura de dias para sempre e eternamente.
Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
5 Grande é a sua gloria pela tua salvação; gloria e magestade pozeste sobre elle.
Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
6 Pois o abençoaste para sempre: tu o enches de gozo com a tua face.
Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
7 Porque o rei confia no Senhor, e pela misericordia do Altissimo nunca vacillará.
Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
8 A tua mão alcançará todos os teus inimigos, a tua mão direita alcançará aquelles que te aborrecem.
Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
9 Tu os farás como um forno de fogo no tempo da tua ira; o Senhor os devorará na sua indignação, e o fogo os consumirá.
A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
10 Seu fructo destruirás da terra, e a sua semente d'entre os filhos dos homens.
Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
11 Porque intentaram o mal contra ti; machinaram uma trapaça, mas não prevalecerão.
Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
12 Portanto tu lhes farás voltar as costas; e com tuas frechas postas nas cordas lhes apontarás ao rosto.
gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
13 Exalta-te, Senhor, na tua força; então cantaremos e louvaremos o teu poder.
Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.

< Salmos 21 >