< Lucas 1 >

1 Tendo pois muitos emprehendido pôr em ordem a narração das coisas que entre nós se cumpriram,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Segundo nos transmittiram os mesmos que as viram desde o principio, e foram ministros da palavra,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Pareceu-me tambem a mim conveniente escrevel-as a ti, ó excellente Theophilo, por sua ordem, havendo-me já informado minuciosamente de tudo desde o principio;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Para que conheças a certeza das coisas de que já estás informado.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Existiu, no tempo de Herodes, rei da Judéa, um sacerdote chamado Zacharias, da ordem de Abias, e cuja mulher era das filhas d'Aarão; e o seu nome era Isabel.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 E eram ambos justos perante Deus, andando sem reprehensão em todos os mandamentos e preceitos do Senhor.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 E não tinham filhos, porquanto Isabel era esteril, e ambos eram avançados em edade.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 E aconteceu que, exercendo elle o sacerdocio diante de Deus, na ordem da sua turma,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Segundo o costume sacerdotal, coube-lhe em sorte entrar no templo do Senhor a offerecer o incenso.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 E toda a multidão do povo estava fóra, orando á hora do incenso,
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 E um anjo do Senhor lhe appareceu, posto em pé, á direita do altar do incenso.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 E Zacharias, vendo-o, turbou-se, e caiu temor sobre elle.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Mas o anjo lhe disse: Zacharias, não temas, porque a tua oração foi ouvida, e Isabel, tua mulher, dará á luz um filho, e lhe porás o nome de João;
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 E terás prazer e alegria, e muitos se alegrarão no seu nascimento;
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Porque será grande diante do Senhor, e não beberá vinho, nem bebida forte, e será cheio do Espirito Sancto, até desde o ventre de sua mãe;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 E converterá muitos dos filhos de Israel ao Senhor seu Deus;
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 E irá adiante d'elle no espirito e virtude d'Elias, para converter os corações dos paes aos filhos, e os rebeldes á prudencia dos justos; para preparar ao Senhor um povo bem disposto.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Disse então Zacharias ao anjo: Como conhecerei isto? pois eu já sou velho, e minha mulher avançada em edade.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 E, respondendo o anjo, disse-lhe: Eu sou Gabriel, que assisto diante de Deus, e fui enviado a fallar-te e dar-te estas alegres novas;
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 E eis que ficarás mudo, e não poderás fallar até ao dia em que estas coisas aconteçam; porquanto não crêste nas minhas palavras, que a seu tempo se hão de cumprir
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 E o povo estava esperando a Zacharias, e maravilhavam-se de que tanto se demorasse no templo.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 E, saindo elle, não lhes podia fallar; e entenderam que tinha visto alguma visão no templo. E fallava por acenos, e ficou mudo.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 E succedeu que, terminados os dias do seu ministerio, voltou para sua casa.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 E depois d'aquelles dias Isabel, sua mulher, concebeu, e por cinco mezes se occultou, dizendo:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Porque isto me fez o Senhor, nos dias em que attentou em mim, para destruir o meu opprobrio entre os homens.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 E, no sexto mez, foi o anjo Gabriel enviado por Deus a uma cidade da Galilea, chamada Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 A uma virgem desposada com um varão, cujo nome era José, da casa de David; e o nome da virgem era Maria.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 E, entrando o anjo aonde ella estava, disse: Salve, agraciada; o Senhor é comtigo: bemdita tu entre as mulheres.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 E, vendo-o ella, turbou-se muito das suas palavras, e considerava que saudação seria esta.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Disse-lhe então o anjo: Maria, não temas, porque achaste graça diante de Deus;
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 E eis que em teu ventre conceberás, e darás á luz um filho, e pôr-lhe-has o nome de Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Este será grande, e será chamado filho do Altissimo; e o Senhor Deus lhe dará o throno de David, seu pae;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 E reinará eternamente na casa de Jacob, e o seu reino não terá fim. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 E disse Maria ao anjo: Como se fará isto? pois não conheço varão.
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 E, respondendo o anjo, disse-lhe: Descerá sobre ti o Espirito Sancto, e a virtude do Altissimo te cobrirá com a sua sombra; pelo que tambem o Sancto, que de ti ha de nascer, será chamado Filho de Deus.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 E eis que tambem Isabel, tua prima, concebeu um filho em sua velhice; e é este o sexto mez para aquella que era chamada esteril;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Porque para Deus nada será impossivel.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Disse então Maria: Eis aqui a serva do Senhor; cumpra-se em mim segundo a tua palavra. E o anjo ausentou-se d'ella.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 E n'aquelles dias, levantando-se Maria, foi apressada ás montanhas, a uma cidade de Juda,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 E entrou em casa de Zacharias, e saudou a Isabel.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 E aconteceu que, ao ouvir Isabel a saudação de Maria, a creancinha saltou no seu ventre; e Isabel foi cheia do Espirito Sancto,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 E exclamou com grande voz, e disse: Bemdita tu entre as mulheres, e bemdito o fructo do teu ventre.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 E d'onde me provém isto a mim, que a mãe do meu Senhor venha a mim?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Pois eis que, ao chegar aos meus ouvidos a voz da tua saudação, a creancinha saltou de alegria no meu ventre;
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 E bemaventurada a que creu, pois hão de cumprir-se as coisas que da parte do Senhor lhe foram ditas.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Disse então Maria: A minha alma engrandece ao Senhor,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 E o meu espirito se alegra em Deus meu Salvador;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Porque attentou na baixeza de sua serva; pois eis que desde agora todas as gerações me chamarão bemaventurada:
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Porque me fez grandes coisas o Poderoso; e sancto é o seu nome.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 E a sua misericordia é de geração em geração sobre os que o temem.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Com o seu braço obrou valorosamente: dissipou os soberbos no pensamento de seus corações.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Depoz dos thronos os poderosos, e elevou os humildes.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Encheu de bens os famintos, e despediu vasios os ricos.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Auxiliou a Israel seu servo, recordando-se da sua misericordia;
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 Como fallou a nossos paes, a Abrahão e á sua posteridade, para sempre. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 E Maria ficou com ella quasi tres mezes, e depois voltou para sua casa.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 E completou-se para Isabel o tempo de dar á luz, e teve um filho.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 E os seus visinhos e parentes ouviram que tinha Deus usado para com ella de grande misericordia, e alegraram-se com ella.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 E aconteceu que, ao oitavo dia, vieram circumcidar o menino, e lhe chamavam Zacharias, do nome de seu pae.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 E, respondendo sua mãe, disse: Não, porém será chamado João.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 E disseram-lhe: Ninguem ha na tua parentela que se chame por este nome.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 E perguntaram por acenos ao pae como queria que lhe chamassem.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 E, pedindo elle uma taboinha de escrever, escreveu, dizendo: O seu nome é João. E todos se maravilharam.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 E logo a bocca se lhe abriu, e a lingua se lhe soltou; e fallava, louvando a Deus.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 E veiu temor sobre todos os seus circumvisinhos, e em todas as montanhas da Judea foram divulgadas todas estas coisas.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 E todos os que as ouviam as conservavam em seus corações, dizendo: Quem será pois este menino? E a mão do Senhor estava com elle.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 E Zacharias, seu pae, foi cheio do Espirito Sancto, e prophetizou, dizendo:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Bemdito o Senhor Deus d'Israel, porque visitou e remiu o seu povo,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 E nos levantou uma salvação poderosa na casa de David seu servo,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 Como fallou pela bocca dos seus sanctos prophetas, desde o principio do mundo; (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Que nos livraria dos nossos inimigos e da mão de todos os que nos aborrecem;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Para manifestar misericordia a nossos paes, e lembrar-se do seu sancto concerto,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 E do juramento que jurou a Abrahão nosso pae,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 De conceder-nos que, libertados da mão de nossos inimigos, o serviriamos sem temor,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 Em sanctidade e justiça perante elle, todos os dias da nossa vida.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 E tu, ó menino, serás chamado propheta do Altissimo, porque has de ir adiante da face do Senhor, a preparar os seus caminhos;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Para dar ao seu povo conhecimento da salvação, na remissão dos seus peccados;
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Pelas entranhas da misericordia do nosso Deus, com que o Oriente do alto nos visitou;
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Para alumiar aos que estão assentados em trevas e sombra de morte; a fim de dirigir os nossos pés pelo caminho da paz.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 E o menino crescia, e se robustecia em espirito. E esteve nos desertos até ao dia em que havia de mostrar-se a Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Lucas 1 >