< Hioba 9 >

1 A Hiob odpowiedział:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Doprawdy, wiem, że tak [jest]. Lecz jak człowiek miałby być usprawiedliwiony przed Bogiem?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Gdyby chciał się z nim spierać, nie odpowie mu ani raz na tysiąc.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Ma on mądre serce i potężną siłę. Kto mu się sprzeciwił i powodziło mu się?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 On przenosi góry, a [ludzie] nie zauważają, przewraca je w swoim gniewie.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 On wstrząsa ziemią z jej miejsca i trzęsą się jej filary.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 On rozkaże słońcu i ono nie wschodzi, zamyka też gwiazdy pieczęcią.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 On sam rozciąga niebiosa i kroczy po falach morza.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 On stworzył Niedźwiedzicę, Oriona, Plejady i gwiazdozbiory południa.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 On czyni rzeczy wielkie i niezbadane, cuda, których zliczyć nie można.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Oto przechodzi obok mnie, a nie widzę go; mija mnie, a ja go nie dostrzegam.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Oto gdy zabiera, któż go powstrzyma? Któż mu powie: Co czynisz?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 Gdyby Bóg nie odwrócił swego gniewu, zuchwali pomocnicy upadliby pod nim.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Jakże ja mu odpowiem? [Jakie] słowa wybiorę, aby się z nim spierać?
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Choćbym był sprawiedliwy, nie odpowiedziałbym mu, lecz błagałbym swojego sędziego.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Choćbym go wzywał, a on by się odezwał, jeszcze nie uwierzyłbym, że mnie wysłuchał;
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 Kruszy mnie bowiem burzą i pomnaża moje rany bez powodu.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 Nie pozwala mi odetchnąć, raczej napełnia mnie goryczą.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Jeśli [chodzi] o siłę, oto jest potężny, a jeśli chodzi o sąd, któż mnie przed nim przyprowadzi?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Jeśli się usprawiedliwię, moje usta mnie potępią. Jeśli powiem, że jestem doskonały, to one wykażą, że jestem przewrotny.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Choćbym był doskonały, przecież nie znałbym swojej duszy; gardziłbym swoim życiem.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 Jedno jest [pewne], dlatego powiedziałem: On niszczy [zarówno] doskonałego, [jak] i niegodziwego;
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 Jeśli bicz nagle zabija, śmieje się on z doświadczenia niewinnych.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 Ziemia została wydana w ręce niegodziwego. On zakrywa oblicze sędziów. A jeśli nie on, któż [to czyni]?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 Ale moje dni są szybsze niż goniec, uciekły i nie widziały nic dobrego.
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 Przeminęły jak szybkie łodzie, jak orzeł, który rzuca się na żer.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Jeśli powiem: Zapomnę o swojej skardze, zaniecham swego gniewu i pocieszę się;
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 Wtedy przerażają mnie wszystkie moje cierpienia, bo wiem, że nie uznasz mnie za niewinnego.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Jeśli jestem niegodziwy, to czemu trudzę się na próżno?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Choćbym się umył wodą ze śniegu i oczyścił mydłem swoje ręce;
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 Ty i tak zanurzysz mnie w dole i moje szaty będą się mną brzydzić.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 On bowiem nie jest człowiekiem jak ja, abym śmiał mu odpowiedzieć i abyśmy razem stanęli przed sądem.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 Nie ma między nami rozjemcy, który mógłby położyć rękę na nas obu.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Niech tylko zdejmie ze mnie swoją rózgę, a jego groza niech mnie już nie przeraża;
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 Wtedy będę mówił i nie będę się go bać; ale tak nie jest ze mną.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Hioba 9 >